• English
  • Business News
Monday, June 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Fatan A Hada Kai Wajen Shawo Kan Kalubalen Dake Addabar Duniya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ana Fatan A Hada Kai Wajen Shawo Kan Kalubalen Dake Addabar Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Cikin jawaban da suka gabatar yayin taron shekara-shekara na Boao dake gudana yanzu haka a birnin Boao na lardin Hainan dake kasar Sin, wasu jagororin kasashen waje sun yi kira ga sassan kasa da kasa da su hada karfi da karfe wajen tunkarar kalubalolin dake addabar duniya, tare da aiwatar da manufofin bunkasa tattalin arzikin duniya.

Yayin da yake tsokaci kan hakan, firaministan Singapore Lee Hsien Loong, ya yi maraba da kwazon kasar Sin a fannin ci gaba da bude kofofin tattalin arzikin ta ga duniya, yana mai fatan Sin din za ta ci gaba da goyon bayan cudanyar dukkanin sassan kasa da kasa, da hadin gwiwar shiyyoyi. Kaza lika ya yi fatan ganin samun karin gudummawar dukkanin sassa wajen ingiza bunkasuwar shiyyar da ma duniya baki daya, ta yadda hakan zai amfani nahiyar Asiya da ma sauran yankunan duniya.

  • Boao: Kasar Sin Ta Karfafa Gwiwar Kasa Da Kasa

A nasa bangare kuwa, firaministan Cote d’Ivoire Patrick Achi, cewa ya yi a wannan lokaci ne ma dandalin na Boao ya fi muhimmanci sama da kowane lokaci, duba da cewa kudurorin da aka amincewa ta hanyar hadin gwiwa, da goyon baya tsakanin sassan kasa da kasa yayin dandalin, na da kusanci matuka da burikan nahiyar Afirka da ma na daukacin bil adama.

Ita kuwa babbar daraktar asusun ba da lamuni na duniya IMF, Kristalina Georgieva, cewa ta yi hadin gwiwar sassan kasashen duniya ya riga ya haifar da sauye-sauye ga tattalin arzikin duniya, ta hanyar zurfafa hade kasuwanni, wanda hakan ya kara bunkasa kudaden shiga, da kyautata rayukan al’ummun duniya baki daya. Jami’ar ta ce “Duk da tasirin sassa masu fatan rarrabuwar kai, a yanzu mun san karfin mu ya karu bisa aiki da muke yi tare”.

Sannan mutane da dama daga kasashe daban daban, sun bayyana taron Boao a matsayin wani babban dandali na tattaunawa, wanda ya hada yanayin nahiyar Asiya tare da tasirin sauran sassan duniya. Fatan su shi ne al’ummun kasa da kasa za su rarraba basirar su, da abubuwan da suka amincewa tare, da hada karfi wajen tunkarar kalubalolin duniya karkashin wannan dandali.

Labarai Masu Nasaba

He Lifeng Zai Ziyarci Birtaniya Tare Da Halartar Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka 

Shugaban Xi Da Takwaransa Na Myanmar Sun Mikawa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya

An kuma gudanar da dandali mai taken “zamanantarwa irin ta kasar Sin”, wanda karamin dandali ne karkashin taron na Boao. Mahalarta dandalin sun bayyana yadda kasar Sin ke bin hanya mafi dacewa ta fuskar neman zamanantar da kasa, wanda baya ga taimakawa da hakan ya yi wajen wanzar da babban ci gaban kasar, a hannu guda ya kuma samarwa duniya wani sabon salon zamanantarwa, da raba dabarun hakan ga sauran sassan duniya, da kafa wani ginshiki na dinkewar duniya a nan gaba.

Yayin karamin taro mai lakabin “Zangon gaba na yanar gizo” kuwa, mahalarta zaman sun yi tattaunawa mai zurfi game da salon ci gaba da ake tunkara a zango na gaba na hidimar yanar gizo, da yadda za a iya gina fasahohin amfani da yanar gizo a nan gaba. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Zan Tsoma Baki A Gwamnatin Abba Ba –Kwankwaso

Next Post

Mutum 14 Sun Shiga Hannun ‘Yan Sanda A Kano Kan Aikata Fashi Da Makami

Related

He Lifeng Zai Ziyarci Birtaniya Tare Da Halartar Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka 
Daga Birnin Sin

He Lifeng Zai Ziyarci Birtaniya Tare Da Halartar Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka 

16 hours ago
Shugaban Xi Da Takwaransa Na Myanmar Sun Mikawa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya
Daga Birnin Sin

Shugaban Xi Da Takwaransa Na Myanmar Sun Mikawa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya

17 hours ago
Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar

19 hours ago
Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 
Daga Birnin Sin

Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

21 hours ago
Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

2 days ago
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili
Daga Birnin Sin

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

2 days ago
Next Post
Mutum 14 Sun Shiga Hannun ‘Yan Sanda A Kano Kan Aikata Fashi Da Makami

Mutum 14 Sun Shiga Hannun 'Yan Sanda A Kano Kan Aikata Fashi Da Makami

LABARAI MASU NASABA

Matawalle: Kofarmu Abude Take Idan Gwamna Dauda Lawal Na San Shigowa Jamiyyar APC

Matawalle: Kofarmu Abude Take Idan Gwamna Dauda Lawal Na San Shigowa Jamiyyar APC

June 9, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 11 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina

June 9, 2025
Mutum 3 Sun Rasu, 15 Sun Jikkata A Wani Hadarin Mota A Hanyar Kano

Hatsarin Mota Ya Yi Ajalin Mutane 9 A Jigawa

June 9, 2025
Gwamnatin Gombe Ta Yi Albishir Ɗin Gina Babban Zangon Noma Da Kiwo Ɗauke Da Kasuwar Duniya A Jihar 

Gwamnatin Gombe Ta Yi Albishir Ɗin Gina Babban Zangon Noma Da Kiwo Ɗauke Da Kasuwar Duniya A Jihar 

June 9, 2025
He Lifeng Zai Ziyarci Birtaniya Tare Da Halartar Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka 

He Lifeng Zai Ziyarci Birtaniya Tare Da Halartar Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka 

June 8, 2025
Ndume Ya Gargaɗi Tinubu Kan 2027: “An Taɓa Yi Wa Jonathan Irin Wannan”

Ndume Ya Gargaɗi Tinubu Kan 2027: “An Taɓa Yi Wa Jonathan Irin Wannan”

June 8, 2025
Shugaban Xi Da Takwaransa Na Myanmar Sun Mikawa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya

Shugaban Xi Da Takwaransa Na Myanmar Sun Mikawa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya

June 8, 2025
Kashim Shettima Ya Ƙaddamar Da Shirin Gyaran Kayayyakin Gwamnati A Borno

Kashim Shettima Ya Ƙaddamar Da Shirin Gyaran Kayayyakin Gwamnati A Borno

June 8, 2025
Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar

Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar

June 8, 2025
Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah

June 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.