• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Fatan A Hada Kai Wajen Shawo Kan Kalubalen Dake Addabar Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
Duniya

Cikin jawaban da suka gabatar yayin taron shekara-shekara na Boao dake gudana yanzu haka a birnin Boao na lardin Hainan dake kasar Sin, wasu jagororin kasashen waje sun yi kira ga sassan kasa da kasa da su hada karfi da karfe wajen tunkarar kalubalolin dake addabar duniya, tare da aiwatar da manufofin bunkasa tattalin arzikin duniya.

Yayin da yake tsokaci kan hakan, firaministan Singapore Lee Hsien Loong, ya yi maraba da kwazon kasar Sin a fannin ci gaba da bude kofofin tattalin arzikin ta ga duniya, yana mai fatan Sin din za ta ci gaba da goyon bayan cudanyar dukkanin sassan kasa da kasa, da hadin gwiwar shiyyoyi. Kaza lika ya yi fatan ganin samun karin gudummawar dukkanin sassa wajen ingiza bunkasuwar shiyyar da ma duniya baki daya, ta yadda hakan zai amfani nahiyar Asiya da ma sauran yankunan duniya.

  • Boao: Kasar Sin Ta Karfafa Gwiwar Kasa Da Kasa

A nasa bangare kuwa, firaministan Cote d’Ivoire Patrick Achi, cewa ya yi a wannan lokaci ne ma dandalin na Boao ya fi muhimmanci sama da kowane lokaci, duba da cewa kudurorin da aka amincewa ta hanyar hadin gwiwa, da goyon baya tsakanin sassan kasa da kasa yayin dandalin, na da kusanci matuka da burikan nahiyar Afirka da ma na daukacin bil adama.

Ita kuwa babbar daraktar asusun ba da lamuni na duniya IMF, Kristalina Georgieva, cewa ta yi hadin gwiwar sassan kasashen duniya ya riga ya haifar da sauye-sauye ga tattalin arzikin duniya, ta hanyar zurfafa hade kasuwanni, wanda hakan ya kara bunkasa kudaden shiga, da kyautata rayukan al’ummun duniya baki daya. Jami’ar ta ce “Duk da tasirin sassa masu fatan rarrabuwar kai, a yanzu mun san karfin mu ya karu bisa aiki da muke yi tare”.

Sannan mutane da dama daga kasashe daban daban, sun bayyana taron Boao a matsayin wani babban dandali na tattaunawa, wanda ya hada yanayin nahiyar Asiya tare da tasirin sauran sassan duniya. Fatan su shi ne al’ummun kasa da kasa za su rarraba basirar su, da abubuwan da suka amincewa tare, da hada karfi wajen tunkarar kalubalolin duniya karkashin wannan dandali.

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

An kuma gudanar da dandali mai taken “zamanantarwa irin ta kasar Sin”, wanda karamin dandali ne karkashin taron na Boao. Mahalarta dandalin sun bayyana yadda kasar Sin ke bin hanya mafi dacewa ta fuskar neman zamanantar da kasa, wanda baya ga taimakawa da hakan ya yi wajen wanzar da babban ci gaban kasar, a hannu guda ya kuma samarwa duniya wani sabon salon zamanantarwa, da raba dabarun hakan ga sauran sassan duniya, da kafa wani ginshiki na dinkewar duniya a nan gaba.

Yayin karamin taro mai lakabin “Zangon gaba na yanar gizo” kuwa, mahalarta zaman sun yi tattaunawa mai zurfi game da salon ci gaba da ake tunkara a zango na gaba na hidimar yanar gizo, da yadda za a iya gina fasahohin amfani da yanar gizo a nan gaba. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an
Daga Birnin Sin

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

November 6, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST
Daga Birnin Sin

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya
Daga Birnin Sin

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Next Post
Mutum 14 Sun Shiga Hannun ‘Yan Sanda A Kano Kan Aikata Fashi Da Makami

Mutum 14 Sun Shiga Hannun 'Yan Sanda A Kano Kan Aikata Fashi Da Makami

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

November 6, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.