ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Fatan A Hada Kai Wajen Shawo Kan Kalubalen Dake Addabar Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
Duniya

Cikin jawaban da suka gabatar yayin taron shekara-shekara na Boao dake gudana yanzu haka a birnin Boao na lardin Hainan dake kasar Sin, wasu jagororin kasashen waje sun yi kira ga sassan kasa da kasa da su hada karfi da karfe wajen tunkarar kalubalolin dake addabar duniya, tare da aiwatar da manufofin bunkasa tattalin arzikin duniya.

Yayin da yake tsokaci kan hakan, firaministan Singapore Lee Hsien Loong, ya yi maraba da kwazon kasar Sin a fannin ci gaba da bude kofofin tattalin arzikin ta ga duniya, yana mai fatan Sin din za ta ci gaba da goyon bayan cudanyar dukkanin sassan kasa da kasa, da hadin gwiwar shiyyoyi. Kaza lika ya yi fatan ganin samun karin gudummawar dukkanin sassa wajen ingiza bunkasuwar shiyyar da ma duniya baki daya, ta yadda hakan zai amfani nahiyar Asiya da ma sauran yankunan duniya.

  • Boao: Kasar Sin Ta Karfafa Gwiwar Kasa Da Kasa

A nasa bangare kuwa, firaministan Cote d’Ivoire Patrick Achi, cewa ya yi a wannan lokaci ne ma dandalin na Boao ya fi muhimmanci sama da kowane lokaci, duba da cewa kudurorin da aka amincewa ta hanyar hadin gwiwa, da goyon baya tsakanin sassan kasa da kasa yayin dandalin, na da kusanci matuka da burikan nahiyar Afirka da ma na daukacin bil adama.

ADVERTISEMENT

Ita kuwa babbar daraktar asusun ba da lamuni na duniya IMF, Kristalina Georgieva, cewa ta yi hadin gwiwar sassan kasashen duniya ya riga ya haifar da sauye-sauye ga tattalin arzikin duniya, ta hanyar zurfafa hade kasuwanni, wanda hakan ya kara bunkasa kudaden shiga, da kyautata rayukan al’ummun duniya baki daya. Jami’ar ta ce “Duk da tasirin sassa masu fatan rarrabuwar kai, a yanzu mun san karfin mu ya karu bisa aiki da muke yi tare”.

Sannan mutane da dama daga kasashe daban daban, sun bayyana taron Boao a matsayin wani babban dandali na tattaunawa, wanda ya hada yanayin nahiyar Asiya tare da tasirin sauran sassan duniya. Fatan su shi ne al’ummun kasa da kasa za su rarraba basirar su, da abubuwan da suka amincewa tare, da hada karfi wajen tunkarar kalubalolin duniya karkashin wannan dandali.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

An kuma gudanar da dandali mai taken “zamanantarwa irin ta kasar Sin”, wanda karamin dandali ne karkashin taron na Boao. Mahalarta dandalin sun bayyana yadda kasar Sin ke bin hanya mafi dacewa ta fuskar neman zamanantar da kasa, wanda baya ga taimakawa da hakan ya yi wajen wanzar da babban ci gaban kasar, a hannu guda ya kuma samarwa duniya wani sabon salon zamanantarwa, da raba dabarun hakan ga sauran sassan duniya, da kafa wani ginshiki na dinkewar duniya a nan gaba.

Yayin karamin taro mai lakabin “Zangon gaba na yanar gizo” kuwa, mahalarta zaman sun yi tattaunawa mai zurfi game da salon ci gaba da ake tunkara a zango na gaba na hidimar yanar gizo, da yadda za a iya gina fasahohin amfani da yanar gizo a nan gaba. (Saminu Alhassan)

Duniya
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Mutum 14 Sun Shiga Hannun ‘Yan Sanda A Kano Kan Aikata Fashi Da Makami

Mutum 14 Sun Shiga Hannun 'Yan Sanda A Kano Kan Aikata Fashi Da Makami

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.