• English
  • Business News
Wednesday, September 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Fatan Sakamakon Ganawar Xi Da Biden Zai Taka Rawa Wajen Kyautata Dangantakar Sin Da Amurka

by Sulaiman
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ana Fatan Sakamakon Ganawar Xi Da Biden Zai Taka Rawa Wajen Kyautata Dangantakar Sin Da Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duniya ta kasa kunne ta ji sakamakon tattaunawar da shugabannin tattalin arziki biyu mafi girma a duniya wato shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na Amurka Joe Biden suka yi, a gefen taron kolin kungiyar APEC da ya gudana a ranar 15 ga watan Nuwamba. Shugabannin biyu sun shafe sama da sa’o’i hudu suna tattaunawa kan batutuwan da za su daidaita dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka, wanda a bayyane ta kasance alakar diflomasiyya mafi muhimmanci a duniya a yau.   

An samu kyakkyawar fahimtar juna a tattaunawar. Bangarorin biyu sun sanar da samun ci gaba a fannonin da Amurka ta dade take son kara yin hadin gwiwa da kasar Sin, ciki har da batun samar da sinadarin fentanyl a kasar Sin, gami da sake dawo da tattaunawar soja tsakanin kasashen biyu, wani bangaren da Amurka ke son a tabbatar da cewa an kauce wa rashin fahimtar juna da rikidewa zuwa rikicin soja.

  • Shugaban Kasar Sin Ya Tattauna Da Takwaransa Na Faransa
  • Xi Da Putin Sun Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taron Tattaunawa Tsakanin Manyan Jami’yyun Siyasar Sin Da Rasha

Bangarorin biyu sun fuskanci juna da nufin nuna wa duniya cewa a shirye suke su daidaita dangantakarsu cikin gaskiya. Don haka, kowanensu na cike da kwarin gwiwa wajen bayyana gaskiya da adalci da ci gaba. Kuma hakan ba shakka ya ginu ne bisa sakamakon taron Bali na bara, da kuma goyon bayan ci gaba da harkokin diflomasiyyar da suka gudana a baya-bayan nan, da daidaita matakan aiki kan wasu muhimman batutuwan da suka ambata.

Shugaba Xi, a jawabinsa na bude taron, ya jaddada cewa, duniya na da girmar da kowace kasa za ta gudanar da harkokinta ba tare da kawo tsaiko ga wata kasa ba, kana, nasarar da wata kasa ta samu dama ce ga wata kasa daban, yayin da shugaba Biden shi kuma ya bayyana muhimmancin tabbatar da cewa gasa ba ta nufin rikici.

A ra’ayi na, tattaunawa da sadarwa su ne mabudin cimma daidaiton da ya dace. Matukar za mu iya sarrafa rashin jituwar dake tsakaninmu ta hanyar tattaunawa da sadarwa da kuma fahimtar juna, ina ganin akwai damar nunawa jama’a da duniya cewa za a iya tafiyar da dangantakar wadannan kasashen biyu cikin gaskiya da adalci. Yana da matukar muhimmanci ga bangarorin biyu su mayar da martani ga bukatun duniya ta hanyar mutunta alakar dake tsakaninsu.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

Duniya a halin yanzu tana fama da ainihin rikice-rikice da dama, kama daga rikicin sauyin yanayi da rashin tabbacin tattalin arziki, zuwa rikice-rikicen dake tasowa na rashin wadatar abinci a dalilin rashin tsaro. Wadannan su ne tarin matsalolin da duniya ke fuskanta da ya kamata a warware a cikin wannan karni na 21, kuma zaman lafiya da jituwa tsakanin Amurka da Sin ka iya zama silar daidaituwar wadannan matsaloli.

Kasashen duniya ba sa so a bar su da zabi tsakanin Amurka da Sin. Duniyar da aka gina a kan bangaranci da rarrabuwar kawuna inda Amurka ke jagorantar wani bangare yayin da Sin ke jan ragamar wani bangare ba shi da amfani ga kasashen duniya. Kuma ba zai taimaka wajen warware matsalolin da duniya ke ciki ba. (Muhammed Yahaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotun Daukaka Kara Ta Tabbatar Da Hyacinth A Matsayin Gwamnan Benuwe

Next Post

Ratciffe Na Dab Da Sayen Kashi 25 Na Manchester United

Related

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

2 hours ago
An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar
Daga Birnin Sin

An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

3 hours ago
Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

3 hours ago
Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

4 hours ago
Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

5 hours ago
Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa

8 hours ago
Next Post
Ratciffe Na Dab Da Sayen Kashi 25 Na Manchester United

Ratciffe Na Dab Da Sayen Kashi 25 Na Manchester United

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

September 9, 2025
IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

September 9, 2025
An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

September 9, 2025
Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

September 9, 2025
Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

September 9, 2025
Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

September 9, 2025
Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

September 9, 2025
Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

September 9, 2025
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Babu Shirin Gaggawa Wajen Fara Aiwatar Da Harajin Kashi 5 Na Man Fetur – Minista

September 9, 2025
Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa

Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa

September 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.