• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Fatan Sakamakon Ganawar Xi Da Biden Zai Taka Rawa Wajen Kyautata Dangantakar Sin Da Amurka

by Sulaiman
2 years ago
Xi

Duniya ta kasa kunne ta ji sakamakon tattaunawar da shugabannin tattalin arziki biyu mafi girma a duniya wato shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na Amurka Joe Biden suka yi, a gefen taron kolin kungiyar APEC da ya gudana a ranar 15 ga watan Nuwamba. Shugabannin biyu sun shafe sama da sa’o’i hudu suna tattaunawa kan batutuwan da za su daidaita dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka, wanda a bayyane ta kasance alakar diflomasiyya mafi muhimmanci a duniya a yau.   

An samu kyakkyawar fahimtar juna a tattaunawar. Bangarorin biyu sun sanar da samun ci gaba a fannonin da Amurka ta dade take son kara yin hadin gwiwa da kasar Sin, ciki har da batun samar da sinadarin fentanyl a kasar Sin, gami da sake dawo da tattaunawar soja tsakanin kasashen biyu, wani bangaren da Amurka ke son a tabbatar da cewa an kauce wa rashin fahimtar juna da rikidewa zuwa rikicin soja.

  • Shugaban Kasar Sin Ya Tattauna Da Takwaransa Na Faransa
  • Xi Da Putin Sun Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taron Tattaunawa Tsakanin Manyan Jami’yyun Siyasar Sin Da Rasha

Bangarorin biyu sun fuskanci juna da nufin nuna wa duniya cewa a shirye suke su daidaita dangantakarsu cikin gaskiya. Don haka, kowanensu na cike da kwarin gwiwa wajen bayyana gaskiya da adalci da ci gaba. Kuma hakan ba shakka ya ginu ne bisa sakamakon taron Bali na bara, da kuma goyon bayan ci gaba da harkokin diflomasiyyar da suka gudana a baya-bayan nan, da daidaita matakan aiki kan wasu muhimman batutuwan da suka ambata.

Shugaba Xi, a jawabinsa na bude taron, ya jaddada cewa, duniya na da girmar da kowace kasa za ta gudanar da harkokinta ba tare da kawo tsaiko ga wata kasa ba, kana, nasarar da wata kasa ta samu dama ce ga wata kasa daban, yayin da shugaba Biden shi kuma ya bayyana muhimmancin tabbatar da cewa gasa ba ta nufin rikici.

A ra’ayi na, tattaunawa da sadarwa su ne mabudin cimma daidaiton da ya dace. Matukar za mu iya sarrafa rashin jituwar dake tsakaninmu ta hanyar tattaunawa da sadarwa da kuma fahimtar juna, ina ganin akwai damar nunawa jama’a da duniya cewa za a iya tafiyar da dangantakar wadannan kasashen biyu cikin gaskiya da adalci. Yana da matukar muhimmanci ga bangarorin biyu su mayar da martani ga bukatun duniya ta hanyar mutunta alakar dake tsakaninsu.

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

Duniya a halin yanzu tana fama da ainihin rikice-rikice da dama, kama daga rikicin sauyin yanayi da rashin tabbacin tattalin arziki, zuwa rikice-rikicen dake tasowa na rashin wadatar abinci a dalilin rashin tsaro. Wadannan su ne tarin matsalolin da duniya ke fuskanta da ya kamata a warware a cikin wannan karni na 21, kuma zaman lafiya da jituwa tsakanin Amurka da Sin ka iya zama silar daidaituwar wadannan matsaloli.

Kasashen duniya ba sa so a bar su da zabi tsakanin Amurka da Sin. Duniyar da aka gina a kan bangaranci da rarrabuwar kawuna inda Amurka ke jagorantar wani bangare yayin da Sin ke jan ragamar wani bangare ba shi da amfani ga kasashen duniya. Kuma ba zai taimaka wajen warware matsalolin da duniya ke ciki ba. (Muhammed Yahaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika
Daga Birnin Sin

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

October 16, 2025
Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

October 16, 2025
Gaza
Daga Birnin Sin

Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?

October 16, 2025
Next Post
Ratciffe Na Dab Da Sayen Kashi 25 Na Manchester United

Ratciffe Na Dab Da Sayen Kashi 25 Na Manchester United

LABARAI MASU NASABA

Manzon Allah

Manzon Allah (SAW) Ne Ya Kafa Tushen Wayewar Kai A Duniya

October 17, 2025
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai

Yadda ‘Yan Bindiga Ke Zafafa Hare-hare A Jihohin Arewa Maso Yamma

October 17, 2025
Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka: Ta Bar Baya Da Ƙura

October 17, 2025
Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

October 17, 2025
Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

October 16, 2025
NAWIA

Ranar Abinci Ta Duniya: NAWIA Ta Tallafawa Mata 114  Da Kayan Aikin Gona A Zamfara

October 16, 2025
Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

October 16, 2025
Gaza

Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?

October 16, 2025
Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

October 16, 2025
Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.