• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Rade-Radin Bullar Cutar ‘Diphtheria’ A Garin Potiskum Na Jihar Yobe

by Muhammad Maitela
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Matsalolin Tsaro Sun Kusa Zama Tarihi A Nijeriya– Gwamna Buni
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu majiyoyi a garin Potiskum sun tabbatar da bullar sabuwar cutar nan ta ‘Diphtheria’ a garin, inda a halin yanzu an samu mutuwar yara da dama yayin da aka kwantar da wasu a cibiyoyin kebe majinyata a sibitin garin.

Dr. Umar Chiroma, shi ne mukaddashin babban sakataren hukumar kula da lafiya a matakin farko na jihar Yobe, ya shaida wa wakilinmu cewa, “Lokacin da muka samu rahoton bullar cutar a garin Potiskum a karshen mako, nan take muka hada tawaga zuwa wuraren da abin ya shafa don wayar da kan jama’a tare da dakile yaduwarta cikin al’umma, ”

  • Yanzu-yanzu: Hon. Buba Mashio Ya Zama Sabon Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Yobe
  • ‘Yansanda Sun Cafke Wasu Yara 2 Da Mahaifinsu Kan Kashe Wani Mutum A Yobe

“Duk da a yanzu ba za mu iya bayyana shi a matsayin Diphtheria ba har sai mun dauki samfurin kwayar cutar mun bincika daga nan za mu iya sanar da abin da ake ciki.”

‘’Wasu daga cikin majinyatan sun haura shekaru 30, wasu 14 yayin da wasu kuma ‘yan shekara 12 zuwa 8 ne. Sannan wani abin takaici shi ne, wasu daga cikin majinyata suna daga cikin wadanda suka bijirewa allurar riga-kafi, wanda hakan ya sa ya fi shafar yaran da ba su yi riga-kafin ba.” In ji shi.

Dr. Chiroma ya kara da cewa, ‘’Wasu daga cikin majinyatan sun warke, don haka ba za mu iya tabbatar da cewa cutar Diphtheria ce har sai idan binciken masana ya gano ita ce, ”

Labarai Masu Nasaba

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

“Da safiyar yau Talata na samu labarin bullar cutar daga daraktan da yake kula da wannan shiyya, saboda haka har yanzu ba mu sami adadin mace-macen a hukumance ba.” Cewar Dr. Chiroma.

Unguwanin da abin ya fi kamari sun hada da unguwar Tandari, Misau Road, Sabuwar Sakateriya, Arikime, Ramin Kasa, Boriya, Yuganda da Texaco quarters.

Wata majiya daga cibiyar kebance majinyata na asibitin kwararru da ke Potiskum ta bayyana cewa suna fuskantar karancin magungunan da za su shawo kan lamarin.

Wata majiya ta shaidawa wakilinmu cewa sama da mutum 46 ne aka kwantar a asibitin, inda yara 20 suka mutu a gida tare da karin wasu 4 da suka mutu a asibitin.

Abdullahi Muhammad, daga garin na Potiskum ya ce ‘’Yara da dama sun mutu a gida kafin a kai su asibiti, wannan cuta ce mai saurin kisa.”

‘’Muna kira ga gwamnati da ta gaggauta daukar matakin ceto rayukan jama’a, daga wannan cuta wadda mun lura ta na dauke da zazzabi, tari, kashe jiki da sauransu.”

A nashi bangaren, jami’in kula da riga-kafi na karamar Hukumar Potiskum, Mallam Buba, ya musanta alkaluman wadanda suka mutu ta sanadin cutar, amma ya ce a kalla yara 42 ne ke kwance a asibiti.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DiphtheriaJihar YobePotiskumYobe
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Nijeriya Sun Damu Kan Yadda Kayan Masarufi Ke Tashin Gwauron Zabi

Next Post

Xi Ya Jaddada Bukatar Samar Da Sabon Tsarin Tattalin Arziki Mai Kara Bude Kofa 

Related

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

1 hour ago
Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

7 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

9 hours ago
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja
Manyan Labarai

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

11 hours ago
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
Manyan Labarai

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

13 hours ago
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Manyan Labarai

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

1 day ago
Next Post
Xi Ya Jaddada Bukatar Samar Da Sabon Tsarin Tattalin Arziki Mai Kara Bude Kofa 

Xi Ya Jaddada Bukatar Samar Da Sabon Tsarin Tattalin Arziki Mai Kara Bude Kofa 

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

September 15, 2025
Neja

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.