• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Rade-Radin Bullar Cutar ‘Diphtheria’ A Garin Potiskum Na Jihar Yobe

by Muhammad Maitela
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Matsalolin Tsaro Sun Kusa Zama Tarihi A Nijeriya– Gwamna Buni
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu majiyoyi a garin Potiskum sun tabbatar da bullar sabuwar cutar nan ta ‘Diphtheria’ a garin, inda a halin yanzu an samu mutuwar yara da dama yayin da aka kwantar da wasu a cibiyoyin kebe majinyata a sibitin garin.

Dr. Umar Chiroma, shi ne mukaddashin babban sakataren hukumar kula da lafiya a matakin farko na jihar Yobe, ya shaida wa wakilinmu cewa, “Lokacin da muka samu rahoton bullar cutar a garin Potiskum a karshen mako, nan take muka hada tawaga zuwa wuraren da abin ya shafa don wayar da kan jama’a tare da dakile yaduwarta cikin al’umma, ”

  • Yanzu-yanzu: Hon. Buba Mashio Ya Zama Sabon Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Yobe
  • ‘Yansanda Sun Cafke Wasu Yara 2 Da Mahaifinsu Kan Kashe Wani Mutum A Yobe

“Duk da a yanzu ba za mu iya bayyana shi a matsayin Diphtheria ba har sai mun dauki samfurin kwayar cutar mun bincika daga nan za mu iya sanar da abin da ake ciki.”

‘’Wasu daga cikin majinyatan sun haura shekaru 30, wasu 14 yayin da wasu kuma ‘yan shekara 12 zuwa 8 ne. Sannan wani abin takaici shi ne, wasu daga cikin majinyata suna daga cikin wadanda suka bijirewa allurar riga-kafi, wanda hakan ya sa ya fi shafar yaran da ba su yi riga-kafin ba.” In ji shi.

Dr. Chiroma ya kara da cewa, ‘’Wasu daga cikin majinyatan sun warke, don haka ba za mu iya tabbatar da cewa cutar Diphtheria ce har sai idan binciken masana ya gano ita ce, ”

Labarai Masu Nasaba

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

“Da safiyar yau Talata na samu labarin bullar cutar daga daraktan da yake kula da wannan shiyya, saboda haka har yanzu ba mu sami adadin mace-macen a hukumance ba.” Cewar Dr. Chiroma.

Unguwanin da abin ya fi kamari sun hada da unguwar Tandari, Misau Road, Sabuwar Sakateriya, Arikime, Ramin Kasa, Boriya, Yuganda da Texaco quarters.

Wata majiya daga cibiyar kebance majinyata na asibitin kwararru da ke Potiskum ta bayyana cewa suna fuskantar karancin magungunan da za su shawo kan lamarin.

Wata majiya ta shaidawa wakilinmu cewa sama da mutum 46 ne aka kwantar a asibitin, inda yara 20 suka mutu a gida tare da karin wasu 4 da suka mutu a asibitin.

Abdullahi Muhammad, daga garin na Potiskum ya ce ‘’Yara da dama sun mutu a gida kafin a kai su asibiti, wannan cuta ce mai saurin kisa.”

‘’Muna kira ga gwamnati da ta gaggauta daukar matakin ceto rayukan jama’a, daga wannan cuta wadda mun lura ta na dauke da zazzabi, tari, kashe jiki da sauransu.”

A nashi bangaren, jami’in kula da riga-kafi na karamar Hukumar Potiskum, Mallam Buba, ya musanta alkaluman wadanda suka mutu ta sanadin cutar, amma ya ce a kalla yara 42 ne ke kwance a asibiti.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DiphtheriaJihar YobePotiskumYobe
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Nijeriya Sun Damu Kan Yadda Kayan Masarufi Ke Tashin Gwauron Zabi

Next Post

Xi Ya Jaddada Bukatar Samar Da Sabon Tsarin Tattalin Arziki Mai Kara Bude Kofa 

Related

Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

5 hours ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

12 hours ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

14 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

15 hours ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

23 hours ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

1 day ago
Next Post
Xi Ya Jaddada Bukatar Samar Da Sabon Tsarin Tattalin Arziki Mai Kara Bude Kofa 

Xi Ya Jaddada Bukatar Samar Da Sabon Tsarin Tattalin Arziki Mai Kara Bude Kofa 

LABARAI MASU NASABA

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.