• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Zargin Jami’an Amotekun Da Kashe Matashi Kan 500 A Ondo

by Sadiq
2 years ago
Amotekun

Jami’an hukumar tsaro ta Jihar Ondo da aka fi sani da Amotekun an yi zargin azabtar da wani yaro dan shekara 14 mai suna Ayomide Adeghalu har lahira.

Lamarin ya faru ne a garin Ondo da ke karamar hukumar Ondo ta Yamma.

  • Ba Mu Amince Da Yin Zanga-Zanga Kan Tsare Malaminmu Ba – Daliban Dakta Idris Dutsen Tanshi
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bayar Da Lasisin Bude Jami’ar Koyo Daga Gida Da Karin Wasu 37

Leadership Hausa ta tattaro cewa Ayomide, wanda ke zaune tare da matar mahaifinsa a unguwar Ogbonkowo da ke Odojomu a cikin garin Ondo, kan taban N500 da aka aike shi.

Sai dai an ce matar mahaifinsa ta fusata ne saboda gazawar yaron ya yi bayanin yadda kudin suka bace kuma ta yanke shawarar hukunta shi domin ya bayyana gaskiya.

Wata majiya da ta zanta da wakilinmu da ya nemi a sakaya sunanta, ta ce bayan an yi masa hukunci mai tsanani, an mika yaron ga jami’an Amotekun wadanda suka azabtar da shi don tilasta masa ya bayyana gaskiyar lamarin.

LABARAI MASU NASABA

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

“Yaron matashin ya fuskanci hukuncin da ya dauki tsawon sa’o’i da dama, duk da rokon da matar mahaifinsa ta yi na a saki yaron.

“Daga baya, matar ta mika shi ga jami’an Amotekun, inda aka gana masa azaba. Ya samu rauni sosai. Har zuwa lokacin da aka garzaya da shi asibitin kwararru da ke Ondo, likitocin da ke bakin aiki sun tabbatar da rasuwarsa,” in ji majiyar.

An tattaro cewa daga baya an kai rahoton lamarin a ofishin ‘yansanda na Fagun da ke Ondo, yayin da aka ajiye gawar yaron a dakin ajiyar gawa.

Da take nuna alhinin rasuwar dan nata, mahaifiyar marigayin, Maryamu, ta ce ta rabu mahaifinsa ne shekaru kadan da suka gabata.

Ta bayyana cewa, makwabta ne suka sanar da ita halin rashin lafiyar yaron.

“Na yi mamakin mutuwar Ayomide saboda ya kasance mai hazaka kuma abun kaunata.

“Bai taba korafin wata cuta gare ni ba. Abin bakin ciki ne a gare ni na samu labarin cewa wasu jami’an tsaro sun azabtar da shi wanda ya yi sanadin mutuwarsa har lahira saboda bacewar Naira 500,” in ji ta.

Kokarin da Leadership ta yi don jin ta bakin Mista Adetunji Adeleye, Kwamandan Rundunar Amotekun ya ci tura.

Sai dai wani jami’in hukumar tsaron yankin ya shaida wa wakilinmu cewa tuni aka fara bincike a kan lamarin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi
Manyan Labarai

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
Next Post
An Zartar Wa Masu Safarar Kwaya Hukuncin Kisa A Iran

An Zartar Wa Masu Safarar Kwaya Hukuncin Kisa A Iran

LABARAI MASU NASABA

gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.