• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Zargin Jami’an Amotekun Da Kashe Matashi Kan 500 A Ondo

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Ana Zargin Jami’an Amotekun Da Kashe Matashi Kan 500 A Ondo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’an hukumar tsaro ta Jihar Ondo da aka fi sani da Amotekun an yi zargin azabtar da wani yaro dan shekara 14 mai suna Ayomide Adeghalu har lahira.

Lamarin ya faru ne a garin Ondo da ke karamar hukumar Ondo ta Yamma.

  • Ba Mu Amince Da Yin Zanga-Zanga Kan Tsare Malaminmu Ba – Daliban Dakta Idris Dutsen Tanshi
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bayar Da Lasisin Bude Jami’ar Koyo Daga Gida Da Karin Wasu 37

Leadership Hausa ta tattaro cewa Ayomide, wanda ke zaune tare da matar mahaifinsa a unguwar Ogbonkowo da ke Odojomu a cikin garin Ondo, kan taban N500 da aka aike shi.

Sai dai an ce matar mahaifinsa ta fusata ne saboda gazawar yaron ya yi bayanin yadda kudin suka bace kuma ta yanke shawarar hukunta shi domin ya bayyana gaskiya.

Wata majiya da ta zanta da wakilinmu da ya nemi a sakaya sunanta, ta ce bayan an yi masa hukunci mai tsanani, an mika yaron ga jami’an Amotekun wadanda suka azabtar da shi don tilasta masa ya bayyana gaskiyar lamarin.

Labarai Masu Nasaba

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

“Yaron matashin ya fuskanci hukuncin da ya dauki tsawon sa’o’i da dama, duk da rokon da matar mahaifinsa ta yi na a saki yaron.

“Daga baya, matar ta mika shi ga jami’an Amotekun, inda aka gana masa azaba. Ya samu rauni sosai. Har zuwa lokacin da aka garzaya da shi asibitin kwararru da ke Ondo, likitocin da ke bakin aiki sun tabbatar da rasuwarsa,” in ji majiyar.

An tattaro cewa daga baya an kai rahoton lamarin a ofishin ‘yansanda na Fagun da ke Ondo, yayin da aka ajiye gawar yaron a dakin ajiyar gawa.

Da take nuna alhinin rasuwar dan nata, mahaifiyar marigayin, Maryamu, ta ce ta rabu mahaifinsa ne shekaru kadan da suka gabata.

Ta bayyana cewa, makwabta ne suka sanar da ita halin rashin lafiyar yaron.

“Na yi mamakin mutuwar Ayomide saboda ya kasance mai hazaka kuma abun kaunata.

“Bai taba korafin wata cuta gare ni ba. Abin bakin ciki ne a gare ni na samu labarin cewa wasu jami’an tsaro sun azabtar da shi wanda ya yi sanadin mutuwarsa har lahira saboda bacewar Naira 500,” in ji ta.

Kokarin da Leadership ta yi don jin ta bakin Mista Adetunji Adeleye, Kwamandan Rundunar Amotekun ya ci tura.

Sai dai wani jami’in hukumar tsaron yankin ya shaida wa wakilinmu cewa tuni aka fara bincike a kan lamarin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmotekunBincikeKisaMatashiOndoZargi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Mu Amince Da Yin Zanga-Zanga Kan Tsare Malaminmu Ba – Daliban Dakta Idris Dutsen Tanshi

Next Post

An Zartar Wa Masu Safarar Kwaya Hukuncin Kisa A Iran

Related

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

3 hours ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

5 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

6 hours ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

14 hours ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

18 hours ago
Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka
Manyan Labarai

Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

1 day ago
Next Post
An Zartar Wa Masu Safarar Kwaya Hukuncin Kisa A Iran

An Zartar Wa Masu Safarar Kwaya Hukuncin Kisa A Iran

LABARAI MASU NASABA

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

August 22, 2025
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

August 22, 2025
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

August 22, 2025
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

August 22, 2025
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

August 22, 2025
Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

August 22, 2025
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

August 22, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

August 22, 2025
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.