• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Zargin Jami’an Amotekun Da Kashe Matashi Kan 500 A Ondo

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Ana Zargin Jami’an Amotekun Da Kashe Matashi Kan 500 A Ondo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’an hukumar tsaro ta Jihar Ondo da aka fi sani da Amotekun an yi zargin azabtar da wani yaro dan shekara 14 mai suna Ayomide Adeghalu har lahira.

Lamarin ya faru ne a garin Ondo da ke karamar hukumar Ondo ta Yamma.

  • Ba Mu Amince Da Yin Zanga-Zanga Kan Tsare Malaminmu Ba – Daliban Dakta Idris Dutsen Tanshi
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bayar Da Lasisin Bude Jami’ar Koyo Daga Gida Da Karin Wasu 37

Leadership Hausa ta tattaro cewa Ayomide, wanda ke zaune tare da matar mahaifinsa a unguwar Ogbonkowo da ke Odojomu a cikin garin Ondo, kan taban N500 da aka aike shi.

Sai dai an ce matar mahaifinsa ta fusata ne saboda gazawar yaron ya yi bayanin yadda kudin suka bace kuma ta yanke shawarar hukunta shi domin ya bayyana gaskiya.

Wata majiya da ta zanta da wakilinmu da ya nemi a sakaya sunanta, ta ce bayan an yi masa hukunci mai tsanani, an mika yaron ga jami’an Amotekun wadanda suka azabtar da shi don tilasta masa ya bayyana gaskiyar lamarin.

Labarai Masu Nasaba

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

“Yaron matashin ya fuskanci hukuncin da ya dauki tsawon sa’o’i da dama, duk da rokon da matar mahaifinsa ta yi na a saki yaron.

“Daga baya, matar ta mika shi ga jami’an Amotekun, inda aka gana masa azaba. Ya samu rauni sosai. Har zuwa lokacin da aka garzaya da shi asibitin kwararru da ke Ondo, likitocin da ke bakin aiki sun tabbatar da rasuwarsa,” in ji majiyar.

An tattaro cewa daga baya an kai rahoton lamarin a ofishin ‘yansanda na Fagun da ke Ondo, yayin da aka ajiye gawar yaron a dakin ajiyar gawa.

Da take nuna alhinin rasuwar dan nata, mahaifiyar marigayin, Maryamu, ta ce ta rabu mahaifinsa ne shekaru kadan da suka gabata.

Ta bayyana cewa, makwabta ne suka sanar da ita halin rashin lafiyar yaron.

“Na yi mamakin mutuwar Ayomide saboda ya kasance mai hazaka kuma abun kaunata.

“Bai taba korafin wata cuta gare ni ba. Abin bakin ciki ne a gare ni na samu labarin cewa wasu jami’an tsaro sun azabtar da shi wanda ya yi sanadin mutuwarsa har lahira saboda bacewar Naira 500,” in ji ta.

Kokarin da Leadership ta yi don jin ta bakin Mista Adetunji Adeleye, Kwamandan Rundunar Amotekun ya ci tura.

Sai dai wani jami’in hukumar tsaron yankin ya shaida wa wakilinmu cewa tuni aka fara bincike a kan lamarin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmotekunBincikeKisaMatashiOndoZargi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Mu Amince Da Yin Zanga-Zanga Kan Tsare Malaminmu Ba – Daliban Dakta Idris Dutsen Tanshi

Next Post

An Zartar Wa Masu Safarar Kwaya Hukuncin Kisa A Iran

Related

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano
Manyan Labarai

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

6 hours ago
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

11 hours ago
Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata
Manyan Labarai

Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

15 hours ago
Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama
Manyan Labarai

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

17 hours ago
Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC
Manyan Labarai

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

18 hours ago
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

1 day ago
Next Post
An Zartar Wa Masu Safarar Kwaya Hukuncin Kisa A Iran

An Zartar Wa Masu Safarar Kwaya Hukuncin Kisa A Iran

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.