ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Zargin Jami’an Amotekun Da Kashe Matashi Kan 500 A Ondo

by Sadiq
3 years ago
Amotekun

Jami’an hukumar tsaro ta Jihar Ondo da aka fi sani da Amotekun an yi zargin azabtar da wani yaro dan shekara 14 mai suna Ayomide Adeghalu har lahira.

Lamarin ya faru ne a garin Ondo da ke karamar hukumar Ondo ta Yamma.

  • Ba Mu Amince Da Yin Zanga-Zanga Kan Tsare Malaminmu Ba – Daliban Dakta Idris Dutsen Tanshi
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bayar Da Lasisin Bude Jami’ar Koyo Daga Gida Da Karin Wasu 37

Leadership Hausa ta tattaro cewa Ayomide, wanda ke zaune tare da matar mahaifinsa a unguwar Ogbonkowo da ke Odojomu a cikin garin Ondo, kan taban N500 da aka aike shi.

ADVERTISEMENT

Sai dai an ce matar mahaifinsa ta fusata ne saboda gazawar yaron ya yi bayanin yadda kudin suka bace kuma ta yanke shawarar hukunta shi domin ya bayyana gaskiya.

Wata majiya da ta zanta da wakilinmu da ya nemi a sakaya sunanta, ta ce bayan an yi masa hukunci mai tsanani, an mika yaron ga jami’an Amotekun wadanda suka azabtar da shi don tilasta masa ya bayyana gaskiyar lamarin.

LABARAI MASU NASABA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

“Yaron matashin ya fuskanci hukuncin da ya dauki tsawon sa’o’i da dama, duk da rokon da matar mahaifinsa ta yi na a saki yaron.

“Daga baya, matar ta mika shi ga jami’an Amotekun, inda aka gana masa azaba. Ya samu rauni sosai. Har zuwa lokacin da aka garzaya da shi asibitin kwararru da ke Ondo, likitocin da ke bakin aiki sun tabbatar da rasuwarsa,” in ji majiyar.

An tattaro cewa daga baya an kai rahoton lamarin a ofishin ‘yansanda na Fagun da ke Ondo, yayin da aka ajiye gawar yaron a dakin ajiyar gawa.

Da take nuna alhinin rasuwar dan nata, mahaifiyar marigayin, Maryamu, ta ce ta rabu mahaifinsa ne shekaru kadan da suka gabata.

Ta bayyana cewa, makwabta ne suka sanar da ita halin rashin lafiyar yaron.

“Na yi mamakin mutuwar Ayomide saboda ya kasance mai hazaka kuma abun kaunata.

“Bai taba korafin wata cuta gare ni ba. Abin bakin ciki ne a gare ni na samu labarin cewa wasu jami’an tsaro sun azabtar da shi wanda ya yi sanadin mutuwarsa har lahira saboda bacewar Naira 500,” in ji ta.

Kokarin da Leadership ta yi don jin ta bakin Mista Adetunji Adeleye, Kwamandan Rundunar Amotekun ya ci tura.

Sai dai wani jami’in hukumar tsaron yankin ya shaida wa wakilinmu cewa tuni aka fara bincike a kan lamarin.

MASU ALAKA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
Manyan Labarai

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Next Post
An Zartar Wa Masu Safarar Kwaya Hukuncin Kisa A Iran

An Zartar Wa Masu Safarar Kwaya Hukuncin Kisa A Iran

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.