• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Zargin ‘Yansanda Da Keta Haddin Dan Jarida A Kano

by Sadiq
3 years ago
'Yansanda

Gidan rediyon Premier da ke Jihar Kano, ya yi Allah wadai da cin zarafi da wani jami’in dan sanda ya yi wa ma’aikacinta a lokacin da ya ke daukar rahoto.

Dan jaridar mai suna Muhammad Bello Dabai, ya sha mari, duka da kuma zagi tare kuma da tursasawa daga gurin wani jami’in dan sanda a lokacin da ya ke kokarin daukar hoto domin hada labara.

  • Buhari Ya Ba Ni Tabbacin Za A Gudanar Da Sahihin Zabe A 2023 – Atiku
  • Na Ji Radadin Da Zafin Rasuwar Shehu Malami – Buhari

Manajan sashen labarai na gidan rediyon, Malam Mukhtar Yahaya Usman ya sanar da hakan ga manema labarai.

Yahaya, ya ce tun da farko lamarin ya faru ne bayan da wani mutum da ya ke fuskantar tuhuma a hannun jami’an ‘yansanda ya kubuce musu a lokacin da ake tafe da shi zuwa asibitin Abdullahi Wase da ke birnin Kano domin a duba lafiyarsa.

Sanarwar ta kara da cewa bayan da wanda ake tuhuma ya kubuce sai ya biyo ta gaban gidan rediyon, inda a nan ne mutane su ka cimma masa kafin daga bisani jami’an ‘yansanda su ka karaso su tafi da shi.

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Hakazalika Mukhtar Yahaya ya ce bayan da jami’an ‘yansandan su ka kama wanda su ke tuhumar daga nan ne Muhammad Bello Dabai ya dauko waya domin daukar hoton abin da ya faru, wanda a nan ne wani jami’in dan sandan ya fara zagi tare da marin dan jaridar duk da cewa ya gabatar da kan sa tare da nuna katin shaidar aiki.

Bayan shan mari da duka jami’in dan sandan ya tursasa Muhammad Bello Dabai shiga cikin motarsu tare da kwantar da shi a kasan motar, inda su ka tafi da shi caji ofis su ka tsare shi na wani lokaci.

Ana dai yawan zargin jami’an tsaron kasar nan musamman ‘yansanda da keta hakkin ‘yan adam.

A baya–bayan nan sai da kungiyar kare hakkin bil Adama (Amnesty International), ta ce ana samun yawaitar kai wa ‘yan jaridar Nijeriya samame tare da tsorata su, abin da ya sa ‘yan jaridar ke aiki cikin yanayi na tsoro da firgici.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba
Manyan Labarai

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
Manyan Labarai

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Next Post
Bayan Komawar ‘Yan Wasan Argentina Gida, Gwamnatin Kasar Ta Ayyana Hutu A Kasar

Bayan Komawar 'Yan Wasan Argentina Gida, Gwamnatin Kasar Ta Ayyana Hutu A Kasar

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

November 2, 2025
Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.