ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Zargin ‘Yansanda Da Keta Haddin Dan Jarida A Kano

by Sadiq
4 years ago
'Yansanda

Gidan rediyon Premier da ke Jihar Kano, ya yi Allah wadai da cin zarafi da wani jami’in dan sanda ya yi wa ma’aikacinta a lokacin da ya ke daukar rahoto.

Dan jaridar mai suna Muhammad Bello Dabai, ya sha mari, duka da kuma zagi tare kuma da tursasawa daga gurin wani jami’in dan sanda a lokacin da ya ke kokarin daukar hoto domin hada labara.

  • Buhari Ya Ba Ni Tabbacin Za A Gudanar Da Sahihin Zabe A 2023 – Atiku
  • Na Ji Radadin Da Zafin Rasuwar Shehu Malami – Buhari

Manajan sashen labarai na gidan rediyon, Malam Mukhtar Yahaya Usman ya sanar da hakan ga manema labarai.

ADVERTISEMENT

Yahaya, ya ce tun da farko lamarin ya faru ne bayan da wani mutum da ya ke fuskantar tuhuma a hannun jami’an ‘yansanda ya kubuce musu a lokacin da ake tafe da shi zuwa asibitin Abdullahi Wase da ke birnin Kano domin a duba lafiyarsa.

Sanarwar ta kara da cewa bayan da wanda ake tuhuma ya kubuce sai ya biyo ta gaban gidan rediyon, inda a nan ne mutane su ka cimma masa kafin daga bisani jami’an ‘yansanda su ka karaso su tafi da shi.

LABARAI MASU NASABA

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

Hakazalika Mukhtar Yahaya ya ce bayan da jami’an ‘yansandan su ka kama wanda su ke tuhumar daga nan ne Muhammad Bello Dabai ya dauko waya domin daukar hoton abin da ya faru, wanda a nan ne wani jami’in dan sandan ya fara zagi tare da marin dan jaridar duk da cewa ya gabatar da kan sa tare da nuna katin shaidar aiki.

Bayan shan mari da duka jami’in dan sandan ya tursasa Muhammad Bello Dabai shiga cikin motarsu tare da kwantar da shi a kasan motar, inda su ka tafi da shi caji ofis su ka tsare shi na wani lokaci.

Ana dai yawan zargin jami’an tsaron kasar nan musamman ‘yansanda da keta hakkin ‘yan adam.

A baya–bayan nan sai da kungiyar kare hakkin bil Adama (Amnesty International), ta ce ana samun yawaitar kai wa ‘yan jaridar Nijeriya samame tare da tsorata su, abin da ya sa ‘yan jaridar ke aiki cikin yanayi na tsoro da firgici.

MASU ALAKA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Next Post
Bayan Komawar ‘Yan Wasan Argentina Gida, Gwamnatin Kasar Ta Ayyana Hutu A Kasar

Bayan Komawar 'Yan Wasan Argentina Gida, Gwamnatin Kasar Ta Ayyana Hutu A Kasar

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.