ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Ba Ta Da ‘Yan Takarar Sanata A Mazabun Yobe Ta Arewa Da A’Ibom Ta Arewa —INEC

by Khalid Idris Doya
3 years ago
APC

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta ce, jam’iyyar APC ba ta da ‘yan takara a kujerun ‘yan Majalisar Dattawa masu neman wakiltar mazabar Yobe ta Arewa da mazabar Akwa Ibom ta Arewa Maso Yamma.

Wadannan mazabun dai su ne wadanda aka yi ta muhawara a kansu dangane da cewa Sanata Ahmad Lawan da Godswill Akpabio sun nemi zama ‘yan takara amma kura ta tashi.

  • Zaben Fidda Gwanin PDP: Wike Ya Gurfanar Da Atiku, Tambuwal Da INEC A Gaban Kotu

Babban kwamishina kuma jami’an watsa labarai da ilmantar da masu zabe, Festus Okoye shi ne ya shaida hakan jiya a lokacin da ke magana ta cikin wani shirin gidan talabijin din Channels mai suna ‘Siyasa A Yau’ ya ce hukumar ba ta amince da kowani mutum cikin biyun a matsayin ‘yan takarar mazabun ba.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Hukumar ta fayyace komai cikin sashi na 29 subsection 1 na dokar zabe. Hakki ne na jam’iyya ta mika sunan jerin sunayen ‘yan takarar da suka samu nasara a zabukan cikin gida da aka gudanar ta sahihi kuma ingataccen hanya ga hukumar zabe ta INEC.

“Wadannan mazabun guda biyu. Sun tura wa INEC sunayen mutane biyu kuma ba mutanen da suka samu nasara ta hanyar gudanar da sahihin zaben fitar da gwani ba ne.

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

“Kuma ba mu wallafa bayanansu ba, a haka ake har yanzu.”

Okoye ya ce hukumarsu ba za su fito ta je tana rokon APC ko wata jam’iyya da ta tura mata sunan wani dan takara da ya lashe zaben ta sahihin zaben cikin gida ba.

“Idan jam’iyya ba ta aiko mana da sunan wani dan takara da ya samu nasara ta sahihin zaben fitar da gwani ba, matsalar da ke akwai shine ‘ita wannan jam’iyyar’ ba ta da ‘yan takara a mazabun da hakan ya faru, kuma haka doka ta fayyace.”

Ya kara da cewa sunayen Lawan da Akpabio ne APC ta aike cikin shafin INEC inda ita kuma hukumar ta yi watsi da sunayen tare da kin amincewa da su.

“Matsalar ma shine har zuwa yanzu, APC ba ta da ‘yan takara a wadannan mazabun,” ya ce.

Ya kara da cewa ba aiki ne fitar wa jam’iyyun siyasa ‘yan takara ba, illa iyaka su sanya ido wajen gudanar da zaben fitar da gwani domin tabbatar da cewa wadanda aka tura mata sunayensu su ne suka samu nasara a zabukan cikin gida da aka gudanar ta sahihi kuma ingataccen hanya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja
Manyan Labarai

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su
Manyan Labarai

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Next Post
Ana Ci Gaba Da Samun Karuwar Wakokin Kyamar Musulmi A Indiya

Ana Ci Gaba Da Samun Karuwar Wakokin Kyamar Musulmi A Indiya

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.