Kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC, ya dage taron yakin neman zaben shugaban kasa a Kano sai zuwa bayan wani lokaci.
Tun da farko dai an shirya taron ne a ranar 16 ga Fabrairu, 2023.
- Maniyyata 700 Wadanda Aka Bari A Bara Za Su Fara Tashi A Bana A Kano – Shugaban NAHCON
- Kotun Daukaka Kara Ta Tabbatar Da Sadiq Wali A Matsayin Dan Takarar Gwamnan PDP A Kano
Daraktan hulda da jama’a kuma mai magana da yawun kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC, Festus Keyamo (SAN), ya tabbatar wa wakilinmu a ranar Juma’a cewa an dage taron.
A cikin sakon WhatsApp, Keyamo ya ce, “Eh gaskiya an dage taron.”
Da aka nemi a bayyana dalilin dage yakin zaben, Keyamo ya bayyana cewa, “Gaba daya an sauya jadawalin yakin zaben.”
An shirya taron ne a matsayin wani shiri na yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu da abokin takararsa, Kashim Shettima gabanin zaben ranar 25 ga watan Fabrairu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp