ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Ilimin Iyaye Na Haifar Da Karuwar Yaran Da Ba Su Zuwa Makaranta (1)

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Ilimi

Rashin ilimi tsakanin manya da matasa ya zama wata babbar matsala, wadda har ta sa masana suke ganin irin lamarin ne yake taimkawa wajen karuwar yaran da ba su zuwa makaranta a Nijeriya.

Ilimin manya ana gane shi ne ta kason mutane daga shekara 15 wadanda suke iya karatu da rubutu, tare da fahimtar ‘yar karamar magana a kan rayuwarsu ta yau da kullum.

Gwamnatin tarayya ta kiyasta lamarin wadanda ke da ilimi ya kai kaso 69, wannan ya nuna ke nan kaso 31 har yanzu su  marasa ilimi, wanda kuma hakan yana nuna akwai mutane da yawa da basu da ilimi, wanda kuma hakan na nufin da akwai bukatar akwai abubuwan da suka kamata a yi ko daukar matakai dangane da hakan da zummar samun daidaiton da ake bukatar samu na wani mizani kamar fiye da kaso 90 na wadanda za su kasance masu ilimi.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Tarayya Ita Kadai Ba Za Ta Iya Daukar Dawainiyar Kudaden Ilimi Ba – Minista
  • Gobara Ta Yi Sanadin Mutuwar Iyalan Kwamishinan Ilimi A Kano

Wadannan alkalumma da hukumar kula da kididdiga ta kasa ta fitar ya nuna sashen Arewacin Nijeriya shi ke da yawan al’ummar da basu da ilimi inda Jihar Yobe take mafi kankanta na kaso 7.23, Zamfara 19.16, Katsina na da kaso10.36 sai Sakkwato mai kaso 15.01, yayin da sashen Kudancin Nijeriya ke da yawan masu ilimi inda Jihar Imo ke jagorancin haka da kaso 96. 43, Legas kaso 96.3, Ekiti  kaso 95.79,sai Ribas da take da kaso 95.76.

Wannan kididdigar ta nuna da akwai wagegen gibi tsakanin sassan biyu wanda ya nuna da akwai bukatar a dauki mataki domin a cike shi gibin da ke da shi, na maganin matsalar da ta sa ake samun yara wadanda basu zuwa makaranta a Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

A kokarin ta na cike gibin ko gurbin da ake da shi hukumar kula da Ilimin manya da yaki da jahilci a wani taron da ta kir ana masuruwa da tsaki a Abuja, na yadda za a cimma buri na karuwar masu ilimin da ake bukata.

Da yake jawabi lokacin taron mai taken” matsalolin da ake fuskanta na gano yawan yaran da basu zuwa makaranta da matasa babban sakataren hukumar,Farfesa.Simon Akpama,’ya ce taron na wadanda za su taimaka sun hada kansu ne domin domin bunkasa ilimin yaki da jahilci a Nijeriya.

Ya kara bayanin cewa ba wata maganar boye- boye lamarin rashin ilimi a tsakanin manya da matasa wata hanya ce da matsalar  yawan yaran da basu zuwa makaranta,ta biyo har ta samu wurin da zata boye.

“Bugu da kari  ya kara bayani duk kokarin da ake na ganin an gano bakin zaren,akwai matsalolin da suke samar da karan- tsaye a kokarin da ake na kawo karshen rashin ilimi ko yaki da jahilcin manya da matasa,hakan ke taimakawa wajen karuwar yaran da basu zuwa makaranta.

Ya kara jaddada cewa ganin yadda lamarin yake ne yasa aka ga yafi dacewa inda har aka dauki mataki na maganin ko kawo karshen babbar matsalar da take damun kasa, inda aka dauki matakin ganin  dukkan manya da matasa sun samu dama ta kasancewa masu ilimi bayan sun yaki jahilci.

Yayin da yake karin haske cewa ilimi bai tsaya kawa ikan iya karatu da rubutu ba,kamar yadda yace  “ ilimi wani tubali ne inda ake fara gina gaba, domin yana ba kowa damar bunkasa al’umma da cigaban  wajen samar da abubuwan more rayuwa”.

Babban sakataren yayin da yake bayani kan yadda za a fita daga matsalar kamar yadda yace lamarin yana hannun manya da matasa wadanda gabarasu ke da dama ta samar da ko kawo cigaba, “fatan da ake da ita da muradai ‘yan gida daya ne inda akwai hanyoyin karuwa masu dama in an samu yakar jahilci aka samu ilimi.”

Manufar wannan taron it ace kira ga dukkan masu ruwa da tsaki su taimakawa kokarin da gwamnati take, inda iin aka hadza hannu daya za a iya gamawa da rashin ilimi ko jahilci, a sake saita ko daidaita tunanin manya da matasa su maida hankalinsu wajen bunkasa cigaban Nijeriya.

Akwai abubuwa da yawa wadanda suke taimakawa wajen karuwar jahilci a Nijeriya da suka hada da, jama’a kara yawa suke a Nijeriya, saboda karuwar da al’umma suke yi ne, shi yasa yawan wadanda basu yaki jahilci ba ke karuwa.

Ilimi
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Ilimi

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

July 11, 2026
ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
Ilimi

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

July 3, 2026
Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Next Post
Taron “Zurfafa Gyare-Gyaren Kasar Sin A Sabon Zamani Dama Ce Ga Duniya” Ya Kaddamar Da Jigo Da Zama Na Musamman Ga Kwararru

Taron “Zurfafa Gyare-Gyaren Kasar Sin A Sabon Zamani Dama Ce Ga Duniya” Ya Kaddamar Da Jigo Da Zama Na Musamman Ga Kwararru

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.