• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asalin Abin Da Ya Sa Barayi Suka Kashe Sheikh Albani Kuri

by Yunusa Isa
2 years ago
in Rahotonni
0
Asalin Abin Da Ya Sa Barayi Suka Kashe Sheikh Albani Kuri
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu barayi hudu sun kutsa gidan fitaccen malamin addinin Musuluncin nan Sheikh Ibrahim Halliru Musa da aka fi sani da Albani Kuri cikin daren ranar Laraba inda suka yi masa kisan gilla.

Barayin sun kutsa gidan malamin ne dake Bobona a Anguwar Tabra ta Karamar Hukumar Akko rufe da fuskokinsu, inda suka bukaci ya basu kudi.

  • An Gudanr Da Taron Dadadden Kwamitin Kula Da Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afrika Ta Kudu
  • Birnin Jinhua Na Kara Kyautata Alaka Da Kasashen Afirka

Kakakin rundunar ‘yansanda a Jihar ASP Mahid Muazu Abubakar, ya tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin, yana mai cewa kawo lokacin hada wannan rahoto ba su kama kowa ba kan lamarin, amma bincike na ci gaba da gudana kamar yadda kwamishinan ‘yansandan jihar CP Okua Etim ya ba da umarni.

Mahid Mu’azu ya ce marigayin ya yi kokarin gane daya daga cikin barayin ne ta hanyar yaye fuskarsa dake rufe, lamarin da ya sa suka sassare shi da adda a wuya da kai da kuma baya, har ma da caccaka masa wuka a kirji.

Ficewarsu ke da wuya aka dauke shi zuwa asibiti, amma saboda munanan raunukan da suka yi masa ba a jima da isa asibitin ba ya rasu.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

Shugaban kungiyar Izala a jihar Sheikh Salisu Muhammad Gombe ya yi Allah wadai tare da bayyana takaici kan kisan, yana mai bayyana rashin Sheikh Albani Kuri a matsayin babban rashi ga al’ummar Musulmi baki daya.

Yace suna fatan binciken da jami’an tsaro ke yi zai haifar da da mai ido ta hanyar kamowa da hukunta wadanda suka aikata wannan danyen aika-aika.

Marigayi malamin addinin Musuluncin ya rasu yana da shekaru 46, ya bar mata biyu da ‘ya’ya hudu da mahaifiyarsa da kuma ‘yan uwa da dama.

Tuni dai aka yi jana’izar Marigayi Sheikh Albani Kuri a masallacin Izala da ke Bolari, wadda ya samu halartar dubban jama’a daga nesa da kusa ciki har da gwamnan jihar Muhammadu Inuwa Yahaya.

A baya bayan nan dai ana samun karuwar shiga gidaje da kwacen waya da sauran miyagun laifuka a jihar, lamarin da masharhanta ke danganta shi da rashin ayyukan yi da zaman banza tsakanin matasa.

Suna ganin kara tsaurara tsaro da samarwa matasa abun yi ka iya taimakawa matuka wajen rage matsalar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

De Bruyne Zai Shafe Makonni Yana Jinya Bayan Raunin Da Ya Samu

Next Post

Australia Ta Doke Faransa A Bugun Fanareti Inda Ta Kai Zagayen Kusa Da Na Karshe

Related

Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

7 days ago
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

2 weeks ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

2 weeks ago
'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

2 weeks ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

3 weeks ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

3 weeks ago
Next Post
Australia Ta Doke Faransa A Bugun Fanareti Inda Ta Kai Zagayen Kusa Da Na Karshe

Australia Ta Doke Faransa A Bugun Fanareti Inda Ta Kai Zagayen Kusa Da Na Karshe

LABARAI MASU NASABA

Albani

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

September 19, 2025
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

September 19, 2025
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

September 19, 2025
An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe ÆŠan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe ÆŠan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.