• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asibitin Yariman Bakura Ya Fara Amfana Da Dokar Ta-ɓaci A Sashen Kiwon Lafiyar Zamfara

by Leadership Hausa
1 year ago
in Kiwon Lafiya
0
Asibitin Yariman Bakura Ya Fara Amfana Da Dokar Ta-ɓaci A Sashen Kiwon Lafiyar Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Asibitin Yariman Bakura da ke Gusau ya fara amfana da dokar ta-ɓaci a sashen kiwon lafiya da Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya ayyana sakamakon ƙaddamar da aikin gyara, ingantawa da kuma samar da kayan aiki a asibitin ƙwararrun ɗaya tilo mallakar gwamnatin jihar.

An gudanar da bikin ƙaddamarwar ne a ranar Alhamis da ta gabata a asibitin ƙwararru na Ahmad Sani Yariman Bakura da ke Gusau, babban birnin jihar.

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa ingantawar za ta mayar da asibitin zuwa asibitin koyarwa na jami’ar Jihar Zamfara.

A yayin jawabinsa a wurin taron, Gwamna Lawal ya tabbatar da cewa, gyaran zai inganta tsarin kula da marasa lafiya ta musamman, da ƙara yawan ma’aikatan kiwon lafiya, da kuma inganta tsarin ayyukan, wanda zai haifar da ingantaccen kiwon lafiya.

“Mun zo nan a yau ne domin ƙaddamar da gyare-gyare da kuma samar da kayan aiki na asibitin ƙwararru na Ahmad Sani Yariman Bakura da ke Gusau. Aikin zai kuma ƙunshi samar da kayan aikin jinya ga asibitin. Wannan aiki dai ya biyo bayan ayyana dokar ta-ɓaci ne a fannin kiwon lafiyar jihar, bayan na ilimi.

Labarai Masu Nasaba

Matsalar Tasgadewar Kashin Baya

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

“Wannan babban ƙalubale ne da muka gada a wannan fanni lokacin da muka karɓi ragamar mulkin jihar.

“Asibitin na cikin mawuyacin hali duk da irin rawar da yake takawa wajen samar da ingantattun ayyukan kiwon lafiya ga mazauna da baƙi a jihar bakiɗaya. Yawancin kayan aikinsa sun lalace, wanda hakan ke nuna buƙatar kulawar gaggawa. Bugu da ƙari, asibitin ba shi da isassun kayan aikin ɗakin gwaje-gwaje, wanda ke kawo cikas ga ma’aikatan wajen aiwatar da muhimman hanyoyin gano cututtuka yadda ya kamata.

asibiti

“Manufarmu ba wai don kare lafiya da jin daɗin mazauna jihar da ma’aikatan kiwon lafiya ba ne kawai, sai dai har da magancewa da shawo kan cututtukan da ke yaɗuwa da kuma waɗanda ba sa yaɗuwa.

“Muna da niyyar samar da cikakkiyar tsarin kula da lafiya wanda zai ƙunshi nau’ikan ayyuka masu muhimmanci, gami da samar da magunguna masu muhimmanci, matakan rigakafi, sake fasalin manufofin kiwon lafiya, aiwatar da ƙa’idoji kan tsaftar ruwa da ƙa’idojin tsabtar muhalli, kula da yanayin kiwon lafiya, shirye-shiryen rigakafi, kula da lafiyar mata masu juna biyu, inganta tsarin abinci mai gina jiki gami da ƙarfafa tsarin ba da gudummawar kuɗaɗen kula da lafiya.

“Kamar yadda Asibitin ƙwararru na Yariman Bakura ya kasance shi ne kaɗai cibiyar kula da lafiya mallakar jihar, akwai buƙatar ya samar da kulawa ta musamman da suka shafi haɗaɗɗun matakan jiyya, tare da ba da horo ga ƙananan likitoci da samar da yanayi mai kyau ga ƙwararrun kiwon lafiya da ke gudanar da bincike a fannonin kiwon lafiya daban-daban. Ya zama wajibi mu tabbatar da sake fasalin asibitin. Mun yi niyyar mayar da Yariman Bakura asibitin koyarwa na Jami’ar Jihar Zamfara da zarar an fara Kwalejin Kimiyyar Lafiya.

asibiti

“Abubuwan da za a aiwatar da gyaran a kan su za su haɗa da sabbin gine-gine, faɗaɗawa da inganta gine-ginen da ake da su, gyara gine-ginen da ake da su, da kammala rukunin ginin likitoci, da bunƙasa ɗakin gwaje-gwaje. Haɓaka kayayyakin aiki da inganta cikakken tsarin Kula da Bayanan Asibiti.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AsibitiBunkasaGwamna Dauda LawalGyaraIngantawaYariman bakuraZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Muhimmiyar Takarda Kan Yanke Hukunci Mai Tsanani Kan Masu Yunkurin Balle Taiwan Daga Kasar Sin Ta Bullo Da Wasu Sakwanni Uku

Next Post

Yadda Aka Yi Wa Finidi George Kora Da Hali Daga Aikin Kocin Super Eagles

Related

Matsalar Tasgadewar Kashin Baya
Kiwon Lafiya

Matsalar Tasgadewar Kashin Baya

1 week ago
Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja
Kiwon Lafiya

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

4 weeks ago
Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi
Kiwon Lafiya

Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi

4 weeks ago
Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa
Kiwon Lafiya

Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa

1 month ago
Matsalar Gishiri Ga Lafiyar Zuciya
Kiwon Lafiya

Matsalar Gishiri Ga Lafiyar Zuciya

2 months ago
Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu
Kiwon Lafiya

Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

2 months ago
Next Post
Yadda Aka Yi Wa Finidi George Kora Da Hali Daga Aikin Kocin Super Eagles

Yadda Aka Yi Wa Finidi George Kora Da Hali Daga Aikin Kocin Super Eagles

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.