Manyan shugabannin haɗakar adawa a Nijeriya, ciki har da Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar da Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Nasir El-Rufai, sun haɗu don kafa sabuwar jam’iyya mai suna All Democratic Alliance (ADA).
Sun ce za su yi amfani da wannan sabuwar jam’iyya wajen ƙalubalantar jam’iyyar APC a zaɓen 2027.
- Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
- Sin Ta Jadadda Wajibcin Daukar Jerin Matakan Magance Matsalar Talauci Da Karancin Ci Gaba Da Rikici
Ƙungiyar, wadda ke aiki ƙarƙashin Nigeria National Coalition Group (NNCG), ta riga ta gabatar da buƙatar yin rijista da sabuwar jam’iyyar ga Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC).
Sun aike da takardar neman rijistar ne a ranar 19 ga watan Yuni, 2025, kuma INEC ta karɓa a hukumance a ranar 20 ga watan Yuni.
Shugaban jam’iyyar ADA, Cif Akin Ricketts, da Sakataren rikon ƙwarya, Abdullahi Musa Elayo, ne suka sanya hannu a takardar.
A cikin takardar, ƙungiyar ta bayyana cewa ta yanke shawarar kafa sabuwar jam’iyya maimakon haɗaka da wasu.
Sun bayyana cewa sun zaɓi suna All Democratic Alliance (ADA) kuma taken jam’iyyar shi ne “Justice for All” wato “Adalci ga Kowa.”
Sun kuma haɗa da adireshin babban ofishin jam’iyyar a cikin takardar.
Sun gabatar da wasu muhimman takardu da suka haɗa da tambarin jam’iyya, tsarin kundin mulki, tutar jam’iyyar, da manufofinta.
Tambarin jam’iyyar ya ƙunshi kayan hatsi irin su masara da launuka masu ma’ana.
Kundin tsarin mulki kuma ya ƙunshi manufofi, tsari da dokokin jam’iyyar, bisa ga tsarin dokokin Najeriya da ƙa’idar dimokuraɗiyya ta duniya.
Takardar ta ƙare da girmamawa, inda ta ke roƙon INEC da ta ɗauki mataki na gaba wajen kammala rijistar jam’iyyar.
Sauran manyan ‘yan siyasa da ke cikin wannan haɗaka sun haɗa da Tsohon Gwamnan Jihar Ribas, Rotimi Amaechi, Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa David Mark, da Dakta Umar Ardo, wanda ya kafa ƙungiyar League of Northern Democrats.
A baya, ƙungiyar ta yi la’akari da shiga wata jam’iyya, kamar African Democratic Congress (ADC) da Social Democratic Party (SDP).
Sai dai daga sun fasa bayan sun lura da rikice-rikicen cikin gida da shari’o’i da waɗannan jam’iyyu ke fuskanta.
Saboda haka, suka zaɓi kafa sabuwar jam’iyya da za su fara daga tushe tare da daidaita tsakanin mambobinta.
Yanzu suna jiran matakin da INEC za ta ɗauka yayin da suke shirin tunkarar zaɓen 2027.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp