ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Awanni 72 Da Ficewa Daga Tafiyar Tinubu Da APC, Naja’atu Muhammad Ta Ziyarci Atiku

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Naja'atu

‘Yar gwagwarmayar nan kuma ‘yar siyasa a jihar Kano, Hajiya Naja’atu Muhammad cikin awa 72 da ficewa daga jam’iyyar APC tare da kaurace wa siyasar bangaranci ko ta jam’iyya.

 

Naja’atu, dai ta yi murabus a matsayin daraktan yakin zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu a ranar Alhamis, kwatsam a ranar Lahadi kuma aka ganota ta ziyarci dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar a Abuja inda ta sha alwashin yin gamayya da shi.

ADVERTISEMENT
  • Atiku: ‘Yan Nijeriya, Tsakanin Mulkin PDP Da APC, Wanne Ya Fi Bala’i?

LEADERSHIP Hausa ta labarto cewa a ranar Alhamis dai Naja’atu ta aike da wasikar ficewa daga APC zuwa ga shugaban kungiyar jam’iyyar na kasa Sanata Abdullahi Adamu inda take bayyana masa dalilanta na yin hakan.

 

LABARAI MASU NASABA

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

Kazalika bayanai daban-daban sun yi nuni da cewa a ranar Asabar Naja’atu ta ce ta daina siyasar bangaranci ko jam’iyyar illa iyaka za ta kasance mai bin mutum da cancanta. Sai dai ganinta da aka yi da Atiku tamkar yin amai ne da lashewa

 

‘Yar fafutukar ta nuna cewa jam’iyyun siyasa da suke kasar nan gaba daya ba su da manufofi na daban kuma ‘yan siyasa na iya sanya kowace irin riga domin cimma manufarsa ta kashin kai a kowani lokaci.

 

“Shi ya sa muke ganin ‘yan siyasa na shiga wannan jam’iyyar su fita su koma wata,” ta ce.

 

Sai dai LEADERSHIP ba ta iya tabbatar da cewa ko Hajiya Naja’atu din ta shiga cikin jam’iyyar PDP ba zuwa yanzu ko kuma kawai zallar goyon bayan takarar Atiku Abubakar ta ke yi a zaben 2023.

 

A hirarsa da jaridar LEADERSHIP a ranar Lahadi, Kakakin kwamitin yakin zaben Atiku/Okowa, Sanata Dino Melaye ya tabbatar mana cewa Hajiya Naja’atu Muhammad din ta ziyarci Atiku Abubakar a ranar Lahadi da yammaci.

 

Melaye, wanda aka gano shi cikin hoton ziyarar tare da Naja’atu da Atiku, ya shaida ma wakilinmu cewa ‘yan fafutukar za ta yi magana kan wannan matakin ne a lokacin da ya dace.

Naja'atu
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

MASU ALAKA

ADC Ta Fara Sayar Da Fom Din Takara Kafin Babban Taron Jam’iyya
Siyasa

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

June 9, 2026
A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara
Siyasa

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

June 8, 2026
Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere
Siyasa

Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

June 8, 2026
Next Post
Sinawa ‘Yan Sama Jannati Sun Gabatar Da Gaisuwar Sabuwar Shekara Daga Cibiyar Binciken Sararin Samaniya

Sinawa ‘Yan Sama Jannati Sun Gabatar Da Gaisuwar Sabuwar Shekara Daga Cibiyar Binciken Sararin Samaniya

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.