ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Awanni 72 Da Ficewa Daga Tafiyar Tinubu Da APC, Naja’atu Muhammad Ta Ziyarci Atiku

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Naja'atu

‘Yar gwagwarmayar nan kuma ‘yar siyasa a jihar Kano, Hajiya Naja’atu Muhammad cikin awa 72 da ficewa daga jam’iyyar APC tare da kaurace wa siyasar bangaranci ko ta jam’iyya.

 

Naja’atu, dai ta yi murabus a matsayin daraktan yakin zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu a ranar Alhamis, kwatsam a ranar Lahadi kuma aka ganota ta ziyarci dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar a Abuja inda ta sha alwashin yin gamayya da shi.

ADVERTISEMENT
  • Atiku: ‘Yan Nijeriya, Tsakanin Mulkin PDP Da APC, Wanne Ya Fi Bala’i?

LEADERSHIP Hausa ta labarto cewa a ranar Alhamis dai Naja’atu ta aike da wasikar ficewa daga APC zuwa ga shugaban kungiyar jam’iyyar na kasa Sanata Abdullahi Adamu inda take bayyana masa dalilanta na yin hakan.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

Kazalika bayanai daban-daban sun yi nuni da cewa a ranar Asabar Naja’atu ta ce ta daina siyasar bangaranci ko jam’iyyar illa iyaka za ta kasance mai bin mutum da cancanta. Sai dai ganinta da aka yi da Atiku tamkar yin amai ne da lashewa

 

‘Yar fafutukar ta nuna cewa jam’iyyun siyasa da suke kasar nan gaba daya ba su da manufofi na daban kuma ‘yan siyasa na iya sanya kowace irin riga domin cimma manufarsa ta kashin kai a kowani lokaci.

 

“Shi ya sa muke ganin ‘yan siyasa na shiga wannan jam’iyyar su fita su koma wata,” ta ce.

 

Sai dai LEADERSHIP ba ta iya tabbatar da cewa ko Hajiya Naja’atu din ta shiga cikin jam’iyyar PDP ba zuwa yanzu ko kuma kawai zallar goyon bayan takarar Atiku Abubakar ta ke yi a zaben 2023.

 

A hirarsa da jaridar LEADERSHIP a ranar Lahadi, Kakakin kwamitin yakin zaben Atiku/Okowa, Sanata Dino Melaye ya tabbatar mana cewa Hajiya Naja’atu Muhammad din ta ziyarci Atiku Abubakar a ranar Lahadi da yammaci.

 

Melaye, wanda aka gano shi cikin hoton ziyarar tare da Naja’atu da Atiku, ya shaida ma wakilinmu cewa ‘yan fafutukar za ta yi magana kan wannan matakin ne a lokacin da ya dace.

Naja'atu
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi

MASU ALAKA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Naja'atu
Siyasa

Muna Da Yan Takarar Gwamna A Jihohi 28 Don Shiga Zaben 2027

September 6, 2026
Next Post
Sinawa ‘Yan Sama Jannati Sun Gabatar Da Gaisuwar Sabuwar Shekara Daga Cibiyar Binciken Sararin Samaniya

Sinawa ‘Yan Sama Jannati Sun Gabatar Da Gaisuwar Sabuwar Shekara Daga Cibiyar Binciken Sararin Samaniya

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.