• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Awanni 72 Da Ficewa Daga Tafiyar Tinubu Da APC, Naja’atu Muhammad Ta Ziyarci Atiku

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Siyasa
0
Awanni 72 Da Ficewa Daga Tafiyar Tinubu Da APC, Naja’atu Muhammad Ta Ziyarci Atiku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yar gwagwarmayar nan kuma ‘yar siyasa a jihar Kano, Hajiya Naja’atu Muhammad cikin awa 72 da ficewa daga jam’iyyar APC tare da kaurace wa siyasar bangaranci ko ta jam’iyya.

 

Naja’atu, dai ta yi murabus a matsayin daraktan yakin zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu a ranar Alhamis, kwatsam a ranar Lahadi kuma aka ganota ta ziyarci dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar a Abuja inda ta sha alwashin yin gamayya da shi.

  • Atiku: ‘Yan Nijeriya, Tsakanin Mulkin PDP Da APC, Wanne Ya Fi Bala’i?

LEADERSHIP Hausa ta labarto cewa a ranar Alhamis dai Naja’atu ta aike da wasikar ficewa daga APC zuwa ga shugaban kungiyar jam’iyyar na kasa Sanata Abdullahi Adamu inda take bayyana masa dalilanta na yin hakan.

 

Labarai Masu Nasaba

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A ZaÉ“en 2027 Ba – NNPP

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

Kazalika bayanai daban-daban sun yi nuni da cewa a ranar Asabar Naja’atu ta ce ta daina siyasar bangaranci ko jam’iyyar illa iyaka za ta kasance mai bin mutum da cancanta. Sai dai ganinta da aka yi da Atiku tamkar yin amai ne da lashewa

 

‘Yar fafutukar ta nuna cewa jam’iyyun siyasa da suke kasar nan gaba daya ba su da manufofi na daban kuma ‘yan siyasa na iya sanya kowace irin riga domin cimma manufarsa ta kashin kai a kowani lokaci.

 

“Shi ya sa muke ganin ‘yan siyasa na shiga wannan jam’iyyar su fita su koma wata,” ta ce.

 

Sai dai LEADERSHIP ba ta iya tabbatar da cewa ko Hajiya Naja’atu din ta shiga cikin jam’iyyar PDP ba zuwa yanzu ko kuma kawai zallar goyon bayan takarar Atiku Abubakar ta ke yi a zaben 2023.

 

A hirarsa da jaridar LEADERSHIP a ranar Lahadi, Kakakin kwamitin yakin zaben Atiku/Okowa, Sanata Dino Melaye ya tabbatar mana cewa Hajiya Naja’atu Muhammad din ta ziyarci Atiku Abubakar a ranar Lahadi da yammaci.

 

Melaye, wanda aka gano shi cikin hoton ziyarar tare da Naja’atu da Atiku, ya shaida ma wakilinmu cewa ‘yan fafutukar za ta yi magana kan wannan matakin ne a lokacin da ya dace.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Murnar Shiga Sabuwar Shekarar Zomo Ta Kasar Sin A Fadin Duniya

Next Post

Sinawa ‘Yan Sama Jannati Sun Gabatar Da Gaisuwar Sabuwar Shekara Daga Cibiyar Binciken Sararin Samaniya

Related

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A ZaÉ“en 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A ZaÉ“en 2027 Ba – NNPP

6 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

10 hours ago
Ba A TaÉ“a Nuno Bidiyon Shugaban Jam’iyyarmu Ta ADC Yana Cusa Dala A Aljihu Ba —Dalung
Labarai

Ba A TaÉ“a Nuno Bidiyon Shugaban Jam’iyyarmu Ta ADC Yana Cusa Dala A Aljihu Ba —Dalung

1 day ago
‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

1 day ago
Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC
Siyasa

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

2 days ago
Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu
Siyasa

Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

2 days ago
Next Post
Sinawa ‘Yan Sama Jannati Sun Gabatar Da Gaisuwar Sabuwar Shekara Daga Cibiyar Binciken Sararin Samaniya

Sinawa ‘Yan Sama Jannati Sun Gabatar Da Gaisuwar Sabuwar Shekara Daga Cibiyar Binciken Sararin Samaniya

LABARAI MASU NASABA

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

July 5, 2025
Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A ZaÉ“en 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A ZaÉ“en 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.