ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Atiku: ‘Yan Nijeriya, Tsakanin Mulkin PDP Da APC, Wanne Ya Fi Bala’i?

by Sulaiman
3 years ago
Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya yi kira ga jama’ar Jihar Neja da sauran ‘yan Nijeriya da su tuno da shekaru 16 na mulkin PDP kuma su kwatanta su da shekaru bakwai na mulkin gwamnatin APC da ya kawo matsananciyar damuwa da talauci da rashin tsaro acikin al’ummar Nijeriya. 

 

Daga nan ya yi kira ga ‘ya’yan jihar da ma ‘yan Nijeriya baki ɗaya da su tabbatar sun aje kyakkyawan tarihi da kyautata wa ‘yan baya ta hanyar korar gwamnatin APC ta hanyar ƙin zaɓen dukkan ‘yan takarar ta a zaɓuɓɓukan da za a yi a watan gobe.

ADVERTISEMENT
  • 2023: Atiku Ya Sha Alwashin Ƙara Wa Jihohi Da Ƙananan Hukumomi Ƙarfin Iko

Atiku ya yi wannan kalamin ne a wajen taron yaƙin neman zaɓen PDP da aka yi a Minna, babban birnin Jihar Neja, a ranar Asabar.

 

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Akwai alamun cewa filin Kasuwar Bajekoli da ke unguwar Shango a garin Minna bai taɓa ganin dandazon mutane ba irin wanda ya gani a ranar Asabar wajen karɓar baƙuncin Atiku da Gwamna Arthur Ifeanyi Okowa na Jihar Delta.

 

Rundunar yaƙin neman zaɓen Atiku/Okowa ta isa Minna ne a ranar Asabar inda jama’a su ka yi dafifi domin tarbar su ta yadda filin ya cika ba masaka tsinke.

 

Tun misalin ƙarfe 8 na safe magoya bayan jam’iyyar su ka cika filin Kasuwar Bajekolin, a yayin da wasu kuma su ka nufi babban filin jirgin sama na Minna mai nisan kimanin kilomita daga cikin gari domin tarbar Atiku da Okowa, da kuma sauran manyan baƙi da su ka haɗa da tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Abubakar Bukola Saraki, Gwamna Aminu Waziri Tambuwal na Jihar Sokoto, Gwamnan Jihar Akwa Ibom, Emmanuel Udom, da tsofaffin gwamnoni Boni Haruna na Adamawa, Liyel Imoke na Kuros Riba, Malam Ibrahim Shekarau na Kano, da sauran su da dama.

 

Filin Kasuwar Bajekolin da ke Shango ya cika maƙil da dubban magoya bayan jam’iyyar PDP. Wasu ma daga wajen filin su ka tsaya, wanda hakan ya jawo cinkoson motoci cika a kan manyan hanyoyin Minna.

 

Tsohon gwamnan Neja, Dakta Mu’azu Babangida Aliyu (Talban Minna), wanda shi ne shugaban rundunar yaƙin neman zaɓen PDP a jihar a zaɓen 2023, shi ma ya yi kira ga jama’a da su fitar da APC daga mulkin jihar domin, a cewar sa, ba ta tsinana komai ba sai jawo baƙin ciki da wahala ga jama’a.

 

Sauran waɗanda su ka yi jawabi a taron sun haɗa da mataimakin Atiku a takara, wato Gwamna Okowa, da Shugaban PDP na ƙasa, Dakta Iyorchia Ayu, da Gwamna Aminu Tambuwal, da Dino Melaye, da Gimbiya Rakiya Atiku (maiɗakin Atiku Abubakar) da Sanata Zaynab Kure, da shugaban PDP na Neja, Tanko Beji, da Gwamna Emmanuel Udom na Akwa Ibom, da sauran su, waɗanda kowannen su ya shawarci masu zaɓe a jihar da su fitar da APC daga mulkin jihar da ma tarayya.

 

An ƙawata taron da hawan raƙuma da dawakai da raye-rayen gargajiya da waƙoƙin mawaƙa irin su Naziru Sarkin Waƙa da sauran su.

 

A ƙarshe, Dakta Babangida Aliyu ya shirya wa Atiku da sauran jiga-jigan jam’iyya walimar cin abincin rana a gidan sa.

Atiku
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Wa’adin Canjin Kudi: Buni Ya Nemi CBN Ya Ƙara Wa Jihar Yobe Lokaci

Wa'adin Canjin Kudi: Buni Ya Nemi CBN Ya Ƙara Wa Jihar Yobe Lokaci

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.