• English
  • Business News
Wednesday, July 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (2)

by Idris Aliyu Daudawa
7 months ago
in Ilimi
0
Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (2)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Maida hankali sosai yana da amfani saboda kuwa dole ne su tabbatar da cewar ana gudanar da ayyuka kamar yadda ya dace wato yadda doka ta ayyana ko ta tanadar.Jami’an ilimi akwai bukatar suna  fahimta da ganewa kan al’amuran ilimin fasaha da yadda ake tafiyar da su.

Dole ne su yi kokari wajen koyon amfani da hanyoyi daban- daban nak afar sadarwa ta zamani saboda kuwa hakan zai taimakawa wajen bunkasa tafiyar da ayyukansu na jami’an ilimi ta hanyoyi da yawa.Daga karshe jami’an ilimi su tilastawa kansu son  bunkasa ilimi da kuma ganin sai dalibai sun fara samun ci gaba kan sakamakon abinda suke koyo.Dole ne su kasance misali da karfafawa wasu da basu kwarin gwiwa su ma su kasance sai sun zama gwarzaye a vanagaren ilimi, duk da hakan kuma su kasance suna kokarin ganin sai an samar da tsare- tsare ko manufofi da za su taimakawa dalibai cimma nasara.

  • Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu
  • Hukumar Ilimin Bai Daya Za Ta Gina Dakunan Karatun Zamani A Makarantun Nijeriya

Kacokan, irin ilimin da ake bukatar jami’in / jami’an ilimi su kasance ya kasance sun san fannoni ko vangarori na ilimi,gogewa ko kwarewa, dabaru da kuma son lamarin aikin nasu har ga zuciya. Irin aiki ko gudunmawa da jami’an ilimi suke badawa bata wuce su tabbatar da cewa dalibai suna samun nagartaccen ingantaccen ilimi,su kuma hukumomin ilimi da al’umma su rika bada tasu gudunmawar bayan suma an taimaka masu domin a cimma muradan ci gaba da ingancin ilimi.

Ci Gaba Kan Ayyukan Jami’in Ilimi

Shi/su jami’an ilimi wadansu mutane ne da yakamata su da lamarin gudanar da ilimi har da tsare- tsare da manufofi a wata makaranta ko hukuma ana tafiyar da su kamar yadda ya dace. Hakanan ma ya dace su tabbatar da cewa  cigaban tsarin manhajar koyarwa, koyon yadda ake koyarwa, irin sakamakon yadda dalibai suke koyo yana tafiya daidai da muradu, manufofin ita hukumar.Jami’an ilimi suna aiki da Malamai, masu tafiyar da lamarin ilimi,da sauran masu fada aji wajen samar da tsare- tsare da manufofi wadanda za su taimaka wajen bunkasa samuwar ingantaccen iulimi ga dalibai.daya daga cikin ayyukan jami’/ jamai’an ilimi shi ne na samar da aiwatar da tsare- tsaren ilimi, wadanda suke taimakawa muradan ko manufofin hukumar.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba

‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato

Wannan ya hada da yadda zai rika yin aiki yana tuntuvar Malamai da sauran  kwararru ta  fannin ilimi domin tabbatar muradan koyarwa, abubuwan ko daraussan da ake koyarwa, da yadda ake auna fahimtar daliban kan abinda aka koya masu, hakan ya yi daidai da abubuwan da su daliban suke son ko, ya kamata  a koya masu da kuma ita hukumar makarantar.Hakanan ma jami’an iimin suna bibyar yadda ake aiwatar da tasare- tsare da manufofi,su kuma  bada shawarwari yadda za a kara bunkasa lamarin, wannan kuma ya dogara ne kan irin bayanan da suka samu daga Malamai, dalibai, da sauran masu ruwa da tsaki .Akwai ma wani babban aikin jami’an ilimi wanda shi ne su bada dama yadda za a samu ci gaban Malamai, da sauaran kwararru ta vangaren ilimi.

Wannan ya kunshi shirya tarurrukan karawa juna ilimi,zuwa wasu muhimman taro, da horarwa lokaci zuwa lokaci wanda hakan zai sa a maida hankali ga sababbin hanyoyin koyarwa, bunkasa manhajojin da za a koyar, da irin dabarar da za ayi amfani da ita  wajen  lura da irin ci gaban da aka samu  sanadiyar hakan.Jami’an ilimi suna bada tsarin koyarwa domin taimakawa Malamai wadanda watakila su kan fuskanci matsala wajen aikinsu na koyarwa, kamar yadda za su iya tafiyar da aji da  kuma sa dalibai su kasance cikin koyarwar.Duk da hakan jami’an ilimi s uke da alhakin lura da yadda ko tsare- tsaren ilimin da manufofin sun dace da yadda ake so ko bukata.

Irin hakan ya hada da sanin yadda fahimtar ko kokarin daliban yake da kuma yin wani abu kan hakan, mai da hankalin Malami kan aikin shin a koyarwa, da sauran abubuwan da suke da alaka da samun nasarar ilimin da ake koyarwa. La’akari da hakan, suna iya bada shawarwari saboda a samar da sauye- sauye kan tsare tsare da manufofi, ko kuma su samar da sabbin hanyoyin da aka san ko tabbatar da za su bunkasa ganewar abinda ake koyawa dalibai wanda hakan zai sa a samu sakamakon da ake so. A takaice, ayyukan jami’in/jami’an ilimi suna da yawa sun kuma bambanta.Wadannan kwararrun suna bada muhimmiyar gudunmawa wajen tabbatar da cewa su tsare – tsare da manufofin ilimi suna tafiya kafada- kafada da bukatar dalibai da hukuma, su ma  kwararrun fannonin ilimi suna samun irin gudunmawar da suke bukata domin su ma su zama suna gudanar da ayyukansu kamar yadda ya dace.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ilimi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Binciken Jami’ar Bayero Ya Gano A Hoton Yatsa Za A Iya Gane Mai Cutar Daji – Farfesa Darma

Next Post

Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman

Related

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba
Ilimi

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba

4 days ago
‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato
Ilimi

‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato

2 weeks ago
UTME
Ilimi

An Samu Rarrabuwar Kai Kan Makin Shiga Manyan Makarantu

2 weeks ago
Jami’ar Ilorin Ta Karrama Shugabannin JAMB, THISDAY Da Wasu 63 A Bikin Shekara 50
Ilimi

Jami’ar Ilorin Ta Karrama Shugabannin JAMB, THISDAY Da Wasu 63 A Bikin Shekara 50

2 weeks ago
Ƴansanda Sun Kama Ɗalibai 11 Kan Kisan Wasu Ɗalibai 2 A Kano
Ilimi

Ƴansanda Sun Kama Ɗalibai 11 Kan Kisan Wasu Ɗalibai 2 A Kano

2 weeks ago
Kwalejin Digiri Na Biyu Ta ABU Ta Ƙaddamar Da Sabbin Ɗalibai A Zariya
Ilimi

Kwalejin Digiri Na Biyu Ta ABU Ta Ƙaddamar Da Sabbin Ɗalibai A Zariya

2 weeks ago
Next Post
Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman

Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana

Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana

July 30, 2025
’Yansanda Sun Gano Gawar Ɗan Jaridar Da Aka Kashe A Jihar Kogi

’Yansanda Sun Gano Gawar Ɗan Jaridar Da Aka Kashe A Jihar Kogi

July 30, 2025
Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa

’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina

July 30, 2025
Shugaban Hukumar Zaɓe Ta Bauchi, Ahmad Makama, Ya Rasu

Shugaban Hukumar Zaɓe Ta Bauchi, Ahmad Makama, Ya Rasu

July 30, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Sauke Kwamishinan Yaɗa Labarai, Ya Maye Gurbinsa Da Maiyaki

Gwamnan Kaduna Ya Sauke Kwamishinan Yaɗa Labarai, Ya Maye Gurbinsa Da Maiyaki

July 30, 2025
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

July 30, 2025
Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

July 30, 2025
Tinubu Ya Nada Ribadu Da Wasu A Matsayin Masu Ba Shi Shawara

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga

July 30, 2025
Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

July 29, 2025
Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

July 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.