• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (2)

by Idris Aliyu Daudawa
8 months ago
in Ilimi
0
Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (2)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Maida hankali sosai yana da amfani saboda kuwa dole ne su tabbatar da cewar ana gudanar da ayyuka kamar yadda ya dace wato yadda doka ta ayyana ko ta tanadar.Jami’an ilimi akwai bukatar suna  fahimta da ganewa kan al’amuran ilimin fasaha da yadda ake tafiyar da su.

Dole ne su yi kokari wajen koyon amfani da hanyoyi daban- daban nak afar sadarwa ta zamani saboda kuwa hakan zai taimakawa wajen bunkasa tafiyar da ayyukansu na jami’an ilimi ta hanyoyi da yawa.Daga karshe jami’an ilimi su tilastawa kansu son  bunkasa ilimi da kuma ganin sai dalibai sun fara samun ci gaba kan sakamakon abinda suke koyo.Dole ne su kasance misali da karfafawa wasu da basu kwarin gwiwa su ma su kasance sai sun zama gwarzaye a vanagaren ilimi, duk da hakan kuma su kasance suna kokarin ganin sai an samar da tsare- tsare ko manufofi da za su taimakawa dalibai cimma nasara.

  • Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu
  • Hukumar Ilimin Bai Daya Za Ta Gina Dakunan Karatun Zamani A Makarantun Nijeriya

Kacokan, irin ilimin da ake bukatar jami’in / jami’an ilimi su kasance ya kasance sun san fannoni ko vangarori na ilimi,gogewa ko kwarewa, dabaru da kuma son lamarin aikin nasu har ga zuciya. Irin aiki ko gudunmawa da jami’an ilimi suke badawa bata wuce su tabbatar da cewa dalibai suna samun nagartaccen ingantaccen ilimi,su kuma hukumomin ilimi da al’umma su rika bada tasu gudunmawar bayan suma an taimaka masu domin a cimma muradan ci gaba da ingancin ilimi.

Ci Gaba Kan Ayyukan Jami’in Ilimi

Shi/su jami’an ilimi wadansu mutane ne da yakamata su da lamarin gudanar da ilimi har da tsare- tsare da manufofi a wata makaranta ko hukuma ana tafiyar da su kamar yadda ya dace. Hakanan ma ya dace su tabbatar da cewa  cigaban tsarin manhajar koyarwa, koyon yadda ake koyarwa, irin sakamakon yadda dalibai suke koyo yana tafiya daidai da muradu, manufofin ita hukumar.Jami’an ilimi suna aiki da Malamai, masu tafiyar da lamarin ilimi,da sauran masu fada aji wajen samar da tsare- tsare da manufofi wadanda za su taimaka wajen bunkasa samuwar ingantaccen iulimi ga dalibai.daya daga cikin ayyukan jami’/ jamai’an ilimi shi ne na samar da aiwatar da tsare- tsaren ilimi, wadanda suke taimakawa muradan ko manufofin hukumar.

Labarai Masu Nasaba

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

Wannan ya hada da yadda zai rika yin aiki yana tuntuvar Malamai da sauran  kwararru ta  fannin ilimi domin tabbatar muradan koyarwa, abubuwan ko daraussan da ake koyarwa, da yadda ake auna fahimtar daliban kan abinda aka koya masu, hakan ya yi daidai da abubuwan da su daliban suke son ko, ya kamata  a koya masu da kuma ita hukumar makarantar.Hakanan ma jami’an iimin suna bibyar yadda ake aiwatar da tasare- tsare da manufofi,su kuma  bada shawarwari yadda za a kara bunkasa lamarin, wannan kuma ya dogara ne kan irin bayanan da suka samu daga Malamai, dalibai, da sauran masu ruwa da tsaki .Akwai ma wani babban aikin jami’an ilimi wanda shi ne su bada dama yadda za a samu ci gaban Malamai, da sauaran kwararru ta vangaren ilimi.

Wannan ya kunshi shirya tarurrukan karawa juna ilimi,zuwa wasu muhimman taro, da horarwa lokaci zuwa lokaci wanda hakan zai sa a maida hankali ga sababbin hanyoyin koyarwa, bunkasa manhajojin da za a koyar, da irin dabarar da za ayi amfani da ita  wajen  lura da irin ci gaban da aka samu  sanadiyar hakan.Jami’an ilimi suna bada tsarin koyarwa domin taimakawa Malamai wadanda watakila su kan fuskanci matsala wajen aikinsu na koyarwa, kamar yadda za su iya tafiyar da aji da  kuma sa dalibai su kasance cikin koyarwar.Duk da hakan jami’an ilimi s uke da alhakin lura da yadda ko tsare- tsaren ilimin da manufofin sun dace da yadda ake so ko bukata.

Irin hakan ya hada da sanin yadda fahimtar ko kokarin daliban yake da kuma yin wani abu kan hakan, mai da hankalin Malami kan aikin shin a koyarwa, da sauran abubuwan da suke da alaka da samun nasarar ilimin da ake koyarwa. La’akari da hakan, suna iya bada shawarwari saboda a samar da sauye- sauye kan tsare tsare da manufofi, ko kuma su samar da sabbin hanyoyin da aka san ko tabbatar da za su bunkasa ganewar abinda ake koyawa dalibai wanda hakan zai sa a samu sakamakon da ake so. A takaice, ayyukan jami’in/jami’an ilimi suna da yawa sun kuma bambanta.Wadannan kwararrun suna bada muhimmiyar gudunmawa wajen tabbatar da cewa su tsare – tsare da manufofin ilimi suna tafiya kafada- kafada da bukatar dalibai da hukuma, su ma  kwararrun fannonin ilimi suna samun irin gudunmawar da suke bukata domin su ma su zama suna gudanar da ayyukansu kamar yadda ya dace.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ilimi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Binciken Jami’ar Bayero Ya Gano A Hoton Yatsa Za A Iya Gane Mai Cutar Daji – Farfesa Darma

Next Post

Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman

Related

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME
Ilimi

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

4 days ago
ASUU
Ilimi

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

5 days ago
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

1 week ago
Lambar Yabo Ta CON: Buni Ya Zama Zinare Bashi Da Maboya
Ilimi

NTIC Ta Jinjina Wa Gwamna Buni Kan Taimako A Bangaren Ilimi

2 weeks ago
Hukumar SUBEB Ta Yi Kira Ga Al’umma Da Su Sa ‘Ya’yansu Makaranta
Ilimi

Hukumar SUBEB Ta Yi Kira Ga Al’umma Da Su Sa ‘Ya’yansu Makaranta

2 weeks ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

3 weeks ago
Next Post
Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman

Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman

LABARAI MASU NASABA

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

September 12, 2025
Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

September 12, 2025
Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

September 12, 2025
Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

September 12, 2025
Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

September 12, 2025
Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

September 12, 2025
Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

September 12, 2025
Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

September 12, 2025
Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

September 12, 2025
Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

September 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.