• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba A Kai Wa Kwankwaso Hari A Kogi Ba – Kungiyar Yakin Zaben Kwankwaso 

by Sadiq
3 years ago
in Siyasa
0
Ba A Kai Wa Kwankwaso Hari A Kogi Ba – Kungiyar Yakin Zaben Kwankwaso 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar yakin neman zaben shugaban kasa ta Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ta musanta rahotannin da kafafen yada labarai suka yada cewa an kai wa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP hari a garin Lokoja a Jihar Kogi.

Wata sanarwa mai dauke da sa hannun kakakin kungiyar yakin neman zaben shugaban kasa na Kwankwaso, Barista Ladipo Johnson, a ranar Alhamis, ta ce rahotannin da ke nuna cewa an kai wa Kwankwaso harin “karya ne, sannan ba su da tushe kuma abin dariya ne.

  • EFCC Ta Cafke Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Ogun
  • An Kashe ‘Yan Boko Haram 49 A Sansaninsu 3 Yayin Luguden Wuta Ta Sama

Johnson ya ce Kwankwaso bai fuskanci komai ba face soyayya daga mutanen Jihar Kogi a ziyarar da ya kai jihar.

Sanarwar ta ce, “An jawo hankalinmu ga rahotanni da dama da kafafen yada labarai suka rika yadawa, wadanda ke nuni da cewa an kai wa ayarin motocin Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP hari a Jihar Kogi.

“Muna so mu bayyana a fili cewar wadannan labaran karya ne, sannan marasa tushe ne kuma abin dariya.

Labarai Masu Nasaba

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

“Tun da ya isa jihar, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso bai samu komai ba face soyayya daga mutanen Jihar Kogi, a ranar Laraba ya ziyarci iyalan abokinsa tsohon gwamnan Jihar Kogi, marigayi Prince Abubakar Audu a wajen taron. Daga nan ne ya zarce zuwa tsakiyar birnin Lokoja domin kaddamar da sabuwar hedikwatar jam’iyyarsa ta jiha.

“Muna so mu bayyana cewa a tsakanin wadannan wurare guda biyu, ayarin motocin dan takarar shugaban kasa babu wani abu da ya same su.

“Bugu da kari, sabanin yadda kafafen yada labarai ke yadawa kan harin da aka ce an kai mana, muna tabbatar da cewa babu wani mai suna Musa Yunusa a cikin tawagar Kwankwaso, saboda haka wannan lamari bai faru ba.

“Kungiyar Kamfen din Kwankwaso na kokarin gurfanar da dan jarida da kuma kafar da suka yada wannan labari.

“Muna kuma kira gare su da suke tabbatar da duk wani labari da ya shafi Rabi’u Musa Kwankwaso, ta bakin masu magana da yawun yakin neman zabensa, su kuma daina yaudarar jama’a, musamman a irin wannan mawuyacin hali.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KogiKungiyar Yakin Neman ZabeKwankwasoLabaran KaryaNNPPSiyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

EFCC Ta Cafke Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Ogun

Next Post

Barawon Da Ke Ihun Kama Barawo

Related

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa
Labarai

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

2 days ago
Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027
Siyasa

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

2 days ago
NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC
Siyasa

NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

3 days ago
Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu
Siyasa

Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

4 days ago
Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP
Siyasa

Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

5 days ago
Dalilin Gwamnatin Kano Na Haramta Shirye-shiryen Siyasa Kai Tsaye
Siyasa

Dalilin Gwamnatin Kano Na Haramta Shirye-shiryen Siyasa Kai Tsaye

1 week ago
Next Post
Barawon Da Ke Ihun Kama Barawo

Barawon Da Ke Ihun Kama Barawo

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.