ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba A Kai Wa Kwankwaso Hari A Kogi Ba – Kungiyar Yakin Zaben Kwankwaso 

by Sadiq
4 years ago
Kwankwaso

Kungiyar yakin neman zaben shugaban kasa ta Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ta musanta rahotannin da kafafen yada labarai suka yada cewa an kai wa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP hari a garin Lokoja a Jihar Kogi.

Wata sanarwa mai dauke da sa hannun kakakin kungiyar yakin neman zaben shugaban kasa na Kwankwaso, Barista Ladipo Johnson, a ranar Alhamis, ta ce rahotannin da ke nuna cewa an kai wa Kwankwaso harin “karya ne, sannan ba su da tushe kuma abin dariya ne.

  • EFCC Ta Cafke Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Ogun
  • An Kashe ‘Yan Boko Haram 49 A Sansaninsu 3 Yayin Luguden Wuta Ta Sama

Johnson ya ce Kwankwaso bai fuskanci komai ba face soyayya daga mutanen Jihar Kogi a ziyarar da ya kai jihar.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta ce, “An jawo hankalinmu ga rahotanni da dama da kafafen yada labarai suka rika yadawa, wadanda ke nuni da cewa an kai wa ayarin motocin Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP hari a Jihar Kogi.

“Muna so mu bayyana a fili cewar wadannan labaran karya ne, sannan marasa tushe ne kuma abin dariya.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

“Tun da ya isa jihar, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso bai samu komai ba face soyayya daga mutanen Jihar Kogi, a ranar Laraba ya ziyarci iyalan abokinsa tsohon gwamnan Jihar Kogi, marigayi Prince Abubakar Audu a wajen taron. Daga nan ne ya zarce zuwa tsakiyar birnin Lokoja domin kaddamar da sabuwar hedikwatar jam’iyyarsa ta jiha.

“Muna so mu bayyana cewa a tsakanin wadannan wurare guda biyu, ayarin motocin dan takarar shugaban kasa babu wani abu da ya same su.

“Bugu da kari, sabanin yadda kafafen yada labarai ke yadawa kan harin da aka ce an kai mana, muna tabbatar da cewa babu wani mai suna Musa Yunusa a cikin tawagar Kwankwaso, saboda haka wannan lamari bai faru ba.

“Kungiyar Kamfen din Kwankwaso na kokarin gurfanar da dan jarida da kuma kafar da suka yada wannan labari.

“Muna kuma kira gare su da suke tabbatar da duk wani labari da ya shafi Rabi’u Musa Kwankwaso, ta bakin masu magana da yawun yakin neman zabensa, su kuma daina yaudarar jama’a, musamman a irin wannan mawuyacin hali.

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Barawon Da Ke Ihun Kama Barawo

Barawon Da Ke Ihun Kama Barawo

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.