ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba A Kai Wa Kwankwaso Hari A Kogi Ba – Kungiyar Yakin Zaben Kwankwaso 

by Sadiq
4 years ago
Kwankwaso

Kungiyar yakin neman zaben shugaban kasa ta Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ta musanta rahotannin da kafafen yada labarai suka yada cewa an kai wa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP hari a garin Lokoja a Jihar Kogi.

Wata sanarwa mai dauke da sa hannun kakakin kungiyar yakin neman zaben shugaban kasa na Kwankwaso, Barista Ladipo Johnson, a ranar Alhamis, ta ce rahotannin da ke nuna cewa an kai wa Kwankwaso harin “karya ne, sannan ba su da tushe kuma abin dariya ne.

  • EFCC Ta Cafke Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Ogun
  • An Kashe ‘Yan Boko Haram 49 A Sansaninsu 3 Yayin Luguden Wuta Ta Sama

Johnson ya ce Kwankwaso bai fuskanci komai ba face soyayya daga mutanen Jihar Kogi a ziyarar da ya kai jihar.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta ce, “An jawo hankalinmu ga rahotanni da dama da kafafen yada labarai suka rika yadawa, wadanda ke nuni da cewa an kai wa ayarin motocin Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP hari a Jihar Kogi.

“Muna so mu bayyana a fili cewar wadannan labaran karya ne, sannan marasa tushe ne kuma abin dariya.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

“Tun da ya isa jihar, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso bai samu komai ba face soyayya daga mutanen Jihar Kogi, a ranar Laraba ya ziyarci iyalan abokinsa tsohon gwamnan Jihar Kogi, marigayi Prince Abubakar Audu a wajen taron. Daga nan ne ya zarce zuwa tsakiyar birnin Lokoja domin kaddamar da sabuwar hedikwatar jam’iyyarsa ta jiha.

“Muna so mu bayyana cewa a tsakanin wadannan wurare guda biyu, ayarin motocin dan takarar shugaban kasa babu wani abu da ya same su.

“Bugu da kari, sabanin yadda kafafen yada labarai ke yadawa kan harin da aka ce an kai mana, muna tabbatar da cewa babu wani mai suna Musa Yunusa a cikin tawagar Kwankwaso, saboda haka wannan lamari bai faru ba.

“Kungiyar Kamfen din Kwankwaso na kokarin gurfanar da dan jarida da kuma kafar da suka yada wannan labari.

“Muna kuma kira gare su da suke tabbatar da duk wani labari da ya shafi Rabi’u Musa Kwankwaso, ta bakin masu magana da yawun yakin neman zabensa, su kuma daina yaudarar jama’a, musamman a irin wannan mawuyacin hali.

MASU ALAKA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Kwankwaso
Siyasa

Muna Da Yan Takarar Gwamna A Jihohi 28 Don Shiga Zaben 2027

September 6, 2026
Next Post
Barawon Da Ke Ihun Kama Barawo

Barawon Da Ke Ihun Kama Barawo

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.