• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba A Kowane Irin Matsayi Zan Iya Fitowa A Cikin Shirin Fim Ba – Isa Bello Ja

by Rabilu Sanusi Bena
9 months ago
Matsayi

Guda daga cikin dattawa a Masana’antar Kannywood, wanda ya shafe fiye da shekara 40 a masana’antar a Nijeriya; Malam Isa Bello Ja (Dattijon Arziki) ya bayyana cewa, ko kadan bai dauki wannan sana’a ta dirama ko wasan kwaikwayo da wasa ba.

Amma hakan, ba zai zama dalilin da zai sa ya yi wani abu da zai zubar masa da mutuncin da ya shafe shekara da shekaru yana nema wa kansa ba. Ya kara da cewa, duk wani abun alheri da mutum zai iya samu a sanadiyar sana’arsa; shi ma ya samu a wannan harka ta wasan kwaikwayo, kama daga zama da manyan mutane masu daraja da mutunci da kuma soyayya da kauna da ya samu daga masoya.

  • Daga Karshe, Yahaya Bello Ya Fada Hannun EFCC
  • Babu Wata Sana’a Da Take Da Daukaka Da Samu Irin Harkar Fim – Hajara Usman 

Amma duk wannan ba zai sa ya fito a matsayin barawo ko dan daudu ko mashayin giya ko kuma mai neman mata ba, domin kuwa tun kafin ya tara iyali yake wannan harka bai yi wani abin ashsha ba; ballantana yanzu da ya tara iyali da surukai da sauran yan’uwa da abokan arziki.

“Tun kafin na shiga harkar fim, na yi aiki a wuraren gwamnati da dama da sauran sana’oi, domin kuwa duk wata sana’a a wajena sana’a ce; don Bahaushe na cewa, babu maraya sai rago, zan iya yin dukkannin wata sana’a don na rufawa kaina asiri, saboda haka, akwai bukatar na tsare mutuncina tare kuma da na sana’ata; wadda nake matukar alfahari da ita”, in ji Ja.

Tun bayan fara wannan sana’a ta dirama da na yi kawo yanzu, zan iya cewa; na yi fina-finai fiye da tunanin mai tunani, daga cikinsu akwai wadanda na fi so fiye da sauran, wadannan kuwa su ne kamar ‘Kowa Ya Bar Gida, Bakan Gizo, Hadarin Kasa da sauran makamantansu, duk wadannan fina-finan ko bayan mutuwata idan aka kalla; babu wanda zai yi tir da ni ko kuma a ce iyalina sun ji kunyar ganina a cikinsu.

LABARAI MASU NASABA

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?

Daga karshe, Bello Ja ya shawarci matasa masu shigowa masana’antar Kannywood; da su dinga tsarkake niyyarsu suna yin aiki tsakaninsu da Allah, sannan kada su yi wani abun ashsha da zai sa a yi wa masu harkar fim kudin goro wajen kiran su da mutanen banza, inda ya ce duk wanda ya jawo aka zagi ‘yan fim, bai kyauta wa mutanen arzikin da ke cikin masana’antar ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 
Nishadi

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

October 11, 2025
Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?
Nishadi

Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?

October 11, 2025
Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano
Nishadi

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

October 6, 2025
Next Post
Ko An Samu Makwafin Mogambo A Fina-finan Indiya Shekara 20 Bayan Mutuwarsa?

Ko An Samu Makwafin Mogambo A Fina-finan Indiya Shekara 20 Bayan Mutuwarsa?

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba

Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba

October 15, 2025
Xi Jinping Ya Taya Patrick Herminie Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Seychelles

Xi Jinping Ya Taya Patrick Herminie Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Seychelles

October 15, 2025
Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

October 15, 2025
Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

October 15, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Barazana Ce Ga Tsaro A Yammacin Afirka – Tinubu

October 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako

October 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Mutum 105, Sun Ƙwato Ƙwayoyi Sama Da 5,000 A Jigawa

October 15, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

October 15, 2025
Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.