• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba A Kowane Irin Matsayi Zan Iya Fitowa A Cikin Shirin Fim Ba – Isa Bello Ja

by Rabilu Sanusi Bena
5 months ago
in Nishadi
0
Ba A Kowane Irin Matsayi Zan Iya Fitowa A Cikin Shirin Fim Ba – Isa Bello Ja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Guda daga cikin dattawa a Masana’antar Kannywood, wanda ya shafe fiye da shekara 40 a masana’antar a Nijeriya; Malam Isa Bello Ja (Dattijon Arziki) ya bayyana cewa, ko kadan bai dauki wannan sana’a ta dirama ko wasan kwaikwayo da wasa ba.

Amma hakan, ba zai zama dalilin da zai sa ya yi wani abu da zai zubar masa da mutuncin da ya shafe shekara da shekaru yana nema wa kansa ba. Ya kara da cewa, duk wani abun alheri da mutum zai iya samu a sanadiyar sana’arsa; shi ma ya samu a wannan harka ta wasan kwaikwayo, kama daga zama da manyan mutane masu daraja da mutunci da kuma soyayya da kauna da ya samu daga masoya.

  • Daga Karshe, Yahaya Bello Ya Fada Hannun EFCC
  • Babu Wata Sana’a Da Take Da Daukaka Da Samu Irin Harkar Fim – Hajara Usman 

Amma duk wannan ba zai sa ya fito a matsayin barawo ko dan daudu ko mashayin giya ko kuma mai neman mata ba, domin kuwa tun kafin ya tara iyali yake wannan harka bai yi wani abin ashsha ba; ballantana yanzu da ya tara iyali da surukai da sauran yan’uwa da abokan arziki.

“Tun kafin na shiga harkar fim, na yi aiki a wuraren gwamnati da dama da sauran sana’oi, domin kuwa duk wata sana’a a wajena sana’a ce; don Bahaushe na cewa, babu maraya sai rago, zan iya yin dukkannin wata sana’a don na rufawa kaina asiri, saboda haka, akwai bukatar na tsare mutuncina tare kuma da na sana’ata; wadda nake matukar alfahari da ita”, in ji Ja.

Tun bayan fara wannan sana’a ta dirama da na yi kawo yanzu, zan iya cewa; na yi fina-finai fiye da tunanin mai tunani, daga cikinsu akwai wadanda na fi so fiye da sauran, wadannan kuwa su ne kamar ‘Kowa Ya Bar Gida, Bakan Gizo, Hadarin Kasa da sauran makamantansu, duk wadannan fina-finan ko bayan mutuwata idan aka kalla; babu wanda zai yi tir da ni ko kuma a ce iyalina sun ji kunyar ganina a cikinsu.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

Daga karshe, Bello Ja ya shawarci matasa masu shigowa masana’antar Kannywood; da su dinga tsarkake niyyarsu suna yin aiki tsakaninsu da Allah, sannan kada su yi wani abun ashsha da zai sa a yi wa masu harkar fim kudin goro wajen kiran su da mutanen banza, inda ya ce duk wanda ya jawo aka zagi ‘yan fim, bai kyauta wa mutanen arzikin da ke cikin masana’antar ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kannywood
ShareTweetSendShare
Previous Post

Na Ɗauki Rarara Tamkar Mahaifi A Wajena – Tijjani Asase

Next Post

Ko An Samu Makwafin Mogambo A Fina-finan Indiya Shekara 20 Bayan Mutuwarsa?

Related

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu
Nishadi

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

5 days ago
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 
Nishadi

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

2 weeks ago
Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani
Nishadi

Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani

3 weeks ago
Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa
Nishadi

Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa

3 weeks ago
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro
Nishadi

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

4 weeks ago
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage
Nishadi

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

4 weeks ago
Next Post
Ko An Samu Makwafin Mogambo A Fina-finan Indiya Shekara 20 Bayan Mutuwarsa?

Ko An Samu Makwafin Mogambo A Fina-finan Indiya Shekara 20 Bayan Mutuwarsa?

LABARAI MASU NASABA

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

June 6, 2025
Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.