• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba A Kowane Irin Matsayi Zan Iya Fitowa A Cikin Shirin Fim Ba – Isa Bello Ja

by Rabilu Sanusi Bena
8 months ago
in Nishadi
0
Ba A Kowane Irin Matsayi Zan Iya Fitowa A Cikin Shirin Fim Ba – Isa Bello Ja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Guda daga cikin dattawa a Masana’antar Kannywood, wanda ya shafe fiye da shekara 40 a masana’antar a Nijeriya; Malam Isa Bello Ja (Dattijon Arziki) ya bayyana cewa, ko kadan bai dauki wannan sana’a ta dirama ko wasan kwaikwayo da wasa ba.

Amma hakan, ba zai zama dalilin da zai sa ya yi wani abu da zai zubar masa da mutuncin da ya shafe shekara da shekaru yana nema wa kansa ba. Ya kara da cewa, duk wani abun alheri da mutum zai iya samu a sanadiyar sana’arsa; shi ma ya samu a wannan harka ta wasan kwaikwayo, kama daga zama da manyan mutane masu daraja da mutunci da kuma soyayya da kauna da ya samu daga masoya.

  • Daga Karshe, Yahaya Bello Ya Fada Hannun EFCC
  • Babu Wata Sana’a Da Take Da Daukaka Da Samu Irin Harkar Fim – Hajara Usman 

Amma duk wannan ba zai sa ya fito a matsayin barawo ko dan daudu ko mashayin giya ko kuma mai neman mata ba, domin kuwa tun kafin ya tara iyali yake wannan harka bai yi wani abin ashsha ba; ballantana yanzu da ya tara iyali da surukai da sauran yan’uwa da abokan arziki.

“Tun kafin na shiga harkar fim, na yi aiki a wuraren gwamnati da dama da sauran sana’oi, domin kuwa duk wata sana’a a wajena sana’a ce; don Bahaushe na cewa, babu maraya sai rago, zan iya yin dukkannin wata sana’a don na rufawa kaina asiri, saboda haka, akwai bukatar na tsare mutuncina tare kuma da na sana’ata; wadda nake matukar alfahari da ita”, in ji Ja.

Tun bayan fara wannan sana’a ta dirama da na yi kawo yanzu, zan iya cewa; na yi fina-finai fiye da tunanin mai tunani, daga cikinsu akwai wadanda na fi so fiye da sauran, wadannan kuwa su ne kamar ‘Kowa Ya Bar Gida, Bakan Gizo, Hadarin Kasa da sauran makamantansu, duk wadannan fina-finan ko bayan mutuwata idan aka kalla; babu wanda zai yi tir da ni ko kuma a ce iyalina sun ji kunyar ganina a cikinsu.

Labarai Masu Nasaba

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

Daga karshe, Bello Ja ya shawarci matasa masu shigowa masana’antar Kannywood; da su dinga tsarkake niyyarsu suna yin aiki tsakaninsu da Allah, sannan kada su yi wani abun ashsha da zai sa a yi wa masu harkar fim kudin goro wajen kiran su da mutanen banza, inda ya ce duk wanda ya jawo aka zagi ‘yan fim, bai kyauta wa mutanen arzikin da ke cikin masana’antar ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kannywood
ShareTweetSendShare
Previous Post

Na Ɗauki Rarara Tamkar Mahaifi A Wajena – Tijjani Asase

Next Post

Ko An Samu Makwafin Mogambo A Fina-finan Indiya Shekara 20 Bayan Mutuwarsa?

Related

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya
Nishadi

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

5 days ago
Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu
Nishadi

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

2 weeks ago
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya
Nishadi

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

2 weeks ago
An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna
Nishadi

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

2 weeks ago
Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ
Nishadi

Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

3 weeks ago
Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami
Nishadi

Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

3 weeks ago
Next Post
Ko An Samu Makwafin Mogambo A Fina-finan Indiya Shekara 20 Bayan Mutuwarsa?

Ko An Samu Makwafin Mogambo A Fina-finan Indiya Shekara 20 Bayan Mutuwarsa?

LABARAI MASU NASABA

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

August 22, 2025
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

August 22, 2025
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

August 22, 2025
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

August 22, 2025
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

August 22, 2025
Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

August 22, 2025
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

August 22, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

August 22, 2025
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.