• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba A Taba Tsareni A Burtaniya Ba, Peter Obi Ya Fayyace Zare Da Abawa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Ba A Taba Tsareni A Burtaniya Ba, Peter Obi Ya Fayyace Zare Da Abawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban kasa a karkashin lemar Labour Party a zaben 2023, Peter Obi, ya fito ya yi bayanin hakikanin abubuwan da suka wakana a tsakaninsu da jami’an hukumar kula da shige da fice a filin sauka da tashin jiragen na kasa da kasa da ke Heathrow a kasar Landan sa’ilin tafiyar da ya yi don bikin Ista. 

 

A hirarsa da Arise News Channel ranar Talata da wakilinmu ya saurara, tsohon gwamnan Jihar Anambra ya fayyace abin da ya fahimta, inda ya ce, jami’an Gwamnatin Burtaniya ba su taba cafke shi balle su tsare shi ba.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Musanta Belin Peter Obi Daga Hannun Birtaniya

Ya ce, abun da ya faru a filin Jirgin Heathrow, wani shigen binciken Immigration ne yayin da ya mika musu shaidarsa domin tantancewa sai suka yi zargin cewa an kwafi shaidarsa ko ironsa guda biyu ne don haka suka bibiyi bayanansa da gano cewa an kwafi irin nasa ne.

 

Labarai Masu Nasaba

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

Obi ya ce, dan tsayar da shi na ‘yan mintina kawai aka yi sabanin bayanan da jam’iyyarsa ta fitar na cewa an dauki tsawon lokaci ana masa tukin tambayoyi.

 

Ya ce: “Sam kwata-kwata ba a kamani ba, ba a tsare ni ba. Sannan, ban aikata kowani irin laifi ba. An tsayar da ni a wurin binciken da aka saba na yau da kullum na hukumar kula da shige da fice saboda bayanan shaidata ya nuna shaida har biyu, kuma dududu bai wuce mintina 20 aka kammala komai.

 

“Ina rayuwa a Burtaniya tun 1993 har zuwa 2005. Daga wancan lokacin zuwa yanzu shekaru 30 kenan. Ba a taba zaunar da ni aka min tuhuma, kamawa ko tsarewa a kowace kasa a fadin duniyar nan. Ban tana samun kaina a bisa wani dalili da aka tuhumeni kan aikata wani laifi ba.

 

“A zahirin gaskiya, shigen binciken ne na yau da kullum, kuma jami’an sun bani dukkanin wata girmamawa sa’ilin da suke min tambayoyi, har ma suka shaida min cewa an kwafi shaidata don haka na kiyaye,” ya shaida.

 

Obi ya kara da cewa duk da yana da cikakken izirin zama a UK, amma ya zabi ya dawo Nijeriya, ya kara da cewa, “Ni haifafen dan Nijeriya ne. Ina kuma son na yi rayuwata a nan na mutu a nan gida Nijeriya”.

 

Ya ce, yana da rubutaccce bayani daga Gwamnatin Burtaniya da ke fayyace cewa ba tsare shi aka yi ba, illa iyaka an tsayar da shi a wurin binciken hukumar shige da fice domin duba bayanan shaidar shige da ficensa na ‘yan mintina kalilan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaɓaɓɓen Gwamnan Zamfara Ya Ziyarci Kasuwar Da Aka Yi Gobara A Gusau

Next Post

Nijeriya Za Ta Yi Koyi Da Salon Ci Gaban Kasar Sin, In Ji Wani Jami’in Kasar

Related

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

2 hours ago
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

4 hours ago
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba
Labarai

Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki

5 hours ago
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

8 hours ago
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

17 hours ago
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu
Labarai

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

19 hours ago
Next Post
Nijeriya Za Ta Yi Koyi Da Salon Ci Gaban Kasar Sin, In Ji Wani Jami’in Kasar

Nijeriya Za Ta Yi Koyi Da Salon Ci Gaban Kasar Sin, In Ji Wani Jami’in Kasar

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

June 30, 2025
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

June 30, 2025
Sin Ta Kalubalanci Kasashen Yammacin Duniya Da Su Tuna Da Laifinsu Na Mulkin Mallaka

Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba

June 30, 2025
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba

Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki

June 30, 2025
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

June 30, 2025
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.