• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba A Taba Tsareni A Burtaniya Ba, Peter Obi Ya Fayyace Zare Da Abawa

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Burtaniya

Dan takarar shugaban kasa a karkashin lemar Labour Party a zaben 2023, Peter Obi, ya fito ya yi bayanin hakikanin abubuwan da suka wakana a tsakaninsu da jami’an hukumar kula da shige da fice a filin sauka da tashin jiragen na kasa da kasa da ke Heathrow a kasar Landan sa’ilin tafiyar da ya yi don bikin Ista. 

 

A hirarsa da Arise News Channel ranar Talata da wakilinmu ya saurara, tsohon gwamnan Jihar Anambra ya fayyace abin da ya fahimta, inda ya ce, jami’an Gwamnatin Burtaniya ba su taba cafke shi balle su tsare shi ba.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Musanta Belin Peter Obi Daga Hannun Birtaniya

Ya ce, abun da ya faru a filin Jirgin Heathrow, wani shigen binciken Immigration ne yayin da ya mika musu shaidarsa domin tantancewa sai suka yi zargin cewa an kwafi shaidarsa ko ironsa guda biyu ne don haka suka bibiyi bayanansa da gano cewa an kwafi irin nasa ne.

 

LABARAI MASU NASABA

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Obi ya ce, dan tsayar da shi na ‘yan mintina kawai aka yi sabanin bayanan da jam’iyyarsa ta fitar na cewa an dauki tsawon lokaci ana masa tukin tambayoyi.

 

Ya ce: “Sam kwata-kwata ba a kamani ba, ba a tsare ni ba. Sannan, ban aikata kowani irin laifi ba. An tsayar da ni a wurin binciken da aka saba na yau da kullum na hukumar kula da shige da fice saboda bayanan shaidata ya nuna shaida har biyu, kuma dududu bai wuce mintina 20 aka kammala komai.

 

“Ina rayuwa a Burtaniya tun 1993 har zuwa 2005. Daga wancan lokacin zuwa yanzu shekaru 30 kenan. Ba a taba zaunar da ni aka min tuhuma, kamawa ko tsarewa a kowace kasa a fadin duniyar nan. Ban tana samun kaina a bisa wani dalili da aka tuhumeni kan aikata wani laifi ba.

 

“A zahirin gaskiya, shigen binciken ne na yau da kullum, kuma jami’an sun bani dukkanin wata girmamawa sa’ilin da suke min tambayoyi, har ma suka shaida min cewa an kwafi shaidata don haka na kiyaye,” ya shaida.

 

Obi ya kara da cewa duk da yana da cikakken izirin zama a UK, amma ya zabi ya dawo Nijeriya, ya kara da cewa, “Ni haifafen dan Nijeriya ne. Ina kuma son na yi rayuwata a nan na mutu a nan gida Nijeriya”.

 

Ya ce, yana da rubutaccce bayani daga Gwamnatin Burtaniya da ke fayyace cewa ba tsare shi aka yi ba, illa iyaka an tsayar da shi a wurin binciken hukumar shige da fice domin duba bayanan shaidar shige da ficensa na ‘yan mintina kalilan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi
Kotu Da Ɗansanda

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma
Manyan Labarai

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP
Labarai

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Next Post
Nijeriya Za Ta Yi Koyi Da Salon Ci Gaban Kasar Sin, In Ji Wani Jami’in Kasar

Nijeriya Za Ta Yi Koyi Da Salon Ci Gaban Kasar Sin, In Ji Wani Jami’in Kasar

LABARAI MASU NASABA

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.