ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba A Taba Tsareni A Burtaniya Ba, Peter Obi Ya Fayyace Zare Da Abawa

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Burtaniya

Dan takarar shugaban kasa a karkashin lemar Labour Party a zaben 2023, Peter Obi, ya fito ya yi bayanin hakikanin abubuwan da suka wakana a tsakaninsu da jami’an hukumar kula da shige da fice a filin sauka da tashin jiragen na kasa da kasa da ke Heathrow a kasar Landan sa’ilin tafiyar da ya yi don bikin Ista. 

 

A hirarsa da Arise News Channel ranar Talata da wakilinmu ya saurara, tsohon gwamnan Jihar Anambra ya fayyace abin da ya fahimta, inda ya ce, jami’an Gwamnatin Burtaniya ba su taba cafke shi balle su tsare shi ba.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Tarayya Ta Musanta Belin Peter Obi Daga Hannun Birtaniya

Ya ce, abun da ya faru a filin Jirgin Heathrow, wani shigen binciken Immigration ne yayin da ya mika musu shaidarsa domin tantancewa sai suka yi zargin cewa an kwafi shaidarsa ko ironsa guda biyu ne don haka suka bibiyi bayanansa da gano cewa an kwafi irin nasa ne.

 

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

Obi ya ce, dan tsayar da shi na ‘yan mintina kawai aka yi sabanin bayanan da jam’iyyarsa ta fitar na cewa an dauki tsawon lokaci ana masa tukin tambayoyi.

 

Ya ce: “Sam kwata-kwata ba a kamani ba, ba a tsare ni ba. Sannan, ban aikata kowani irin laifi ba. An tsayar da ni a wurin binciken da aka saba na yau da kullum na hukumar kula da shige da fice saboda bayanan shaidata ya nuna shaida har biyu, kuma dududu bai wuce mintina 20 aka kammala komai.

 

“Ina rayuwa a Burtaniya tun 1993 har zuwa 2005. Daga wancan lokacin zuwa yanzu shekaru 30 kenan. Ba a taba zaunar da ni aka min tuhuma, kamawa ko tsarewa a kowace kasa a fadin duniyar nan. Ban tana samun kaina a bisa wani dalili da aka tuhumeni kan aikata wani laifi ba.

 

“A zahirin gaskiya, shigen binciken ne na yau da kullum, kuma jami’an sun bani dukkanin wata girmamawa sa’ilin da suke min tambayoyi, har ma suka shaida min cewa an kwafi shaidata don haka na kiyaye,” ya shaida.

 

Obi ya kara da cewa duk da yana da cikakken izirin zama a UK, amma ya zabi ya dawo Nijeriya, ya kara da cewa, “Ni haifafen dan Nijeriya ne. Ina kuma son na yi rayuwata a nan na mutu a nan gida Nijeriya”.

 

Ya ce, yana da rubutaccce bayani daga Gwamnatin Burtaniya da ke fayyace cewa ba tsare shi aka yi ba, illa iyaka an tsayar da shi a wurin binciken hukumar shige da fice domin duba bayanan shaidar shige da ficensa na ‘yan mintina kalilan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

November 15, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026
Labarai

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano
Kotu Da Ɗansanda

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Next Post
Nijeriya Za Ta Yi Koyi Da Salon Ci Gaban Kasar Sin, In Ji Wani Jami’in Kasar

Nijeriya Za Ta Yi Koyi Da Salon Ci Gaban Kasar Sin, In Ji Wani Jami’in Kasar

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

November 15, 2025
Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.