• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Mu Da Shirin Mayar Da Nijeriya Tsarin Jam’iyya Daya —APC

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
APC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakataren jam’iyyar APC na kasa, Sanata Ajibola Bashiru ya bayyana cewa babu wani shiri na bayar da Nijeriya karkashin tsarin jam’iyya daya, amma jam’iyyar za ta ci gaba da lashe zabe a kasar nan.

Ya bayyana hakan ne a lokacin da yake yi wa dimbin magoya bayan jam’iyyar jawabi a sakateriyar jam’iyyar da ke Abuja, wanda suka magoya bayan jam’iyyar suka mamaye shalkwatan domin nuna goyon baya ga shugaban jam’iyyar na kasa, Abdullahi Umar Ganduje.

  • Umarnin Kotu Da Ya Tabbatar Da Dakatar Da Ganduje Bai Inganta Ba, Ba Za Mu Yi Biyayya Ba – APC
  • Garkuwa Da ‘Yan Makaranta: Nijeriya Ba Za Ta Sake Biyan Kuɗin Fansa Ba – Tinubu

Ya ce, “Mu ba mu ce dole sai Nijeriya ta koma tsarin jam’iya daya ba. Amma mun gina jam’iyyar da za ta dunga lashe zabe a ko da yaushe. Muna tabbatar da cewa akwai kudin samar da ilimi da kuma sauran ababen more rayuwa.

“Makiya ba su isa su hana mu ci gaba ba. Muna bayar da goyon baya ga jagoranmu, mai girma Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu bisa yadda yake aiwatar da shirinsa na sake farfado da kasar nan. Muna kara hada kai karkashin jagorancin shugaban jam’iyyarmu na kasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje.”

A kwanan nan dai Ganduje yana fuskantar ce-ce-ku-ce game da dakatar da shi a matsayin shugaban jam’iyyar APC.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

Amma da yake jawabi ga dimbin magoya bayan jam’iyyar, Ganduje ya ce wasu ne kawai suke jin tsoron yadda yake aiwatar da lamuran jam’iyyar, wanda suka kulla masa kutun-gwila.

“Sun jin tsoron yadda muke sulhunta ‘ya’yan jam’iyyar. Suna jin tsoro ne saboda muna samun mutane wadanda suke yin tururuwa wajen shiga jam’iyyar a ko’ina a fadin kasar nan. Wannan shi ya haddasa musu tsoro a zukatansu.

“Suna sa ido a 2027, amma a wannan lokaci babu wani gurbi. Shugaban kasarmu, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ne zai ci gaba da mulkin Nijeriya idan Allah ya yarda.”

Da yake kira ga magoya bayan APC su yi watsi da abun da ya kira dirama, Ganduje ya ce, “Mun fahimci abubuwan da suke yi. Wasan kwaikwayon siyasa ne. Suna yin wannan dirama ne domin su boye gazawarsu. Ba za mu taba barin su ci gaba da wannan ba.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaAPCsiyasar Nijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ranar ‘Yancin ‘Yan Jarida: AMDF Ta Nemi A Bai Wa ‘Yan Jarida Kariya A Afirka

Next Post

Ministan Wajen Hungary Na Fatan Ziyarar Xi Za Ta Bude Sabon Babi Na Dangantakar Hungary Da Sin

Related

Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

51 minutes ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 week ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

2 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

2 weeks ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 month ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 month ago
Next Post
Ministan Wajen Hungary Na Fatan Ziyarar Xi Za Ta Bude Sabon Babi Na Dangantakar Hungary Da Sin

Ministan Wajen Hungary Na Fatan Ziyarar Xi Za Ta Bude Sabon Babi Na Dangantakar Hungary Da Sin

LABARAI MASU NASABA

Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.