Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home LABARAI

Ba Mu Da Wata Matsala A Jihar Enugu -Ardo Baso

by Tayo Adelaja
September 26, 2017
in LABARAI
1 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga A.A.Masagala, Benin

A wata hira da LEADERSHIP A YAU ta yi kwanan nan tare da jagoran Fulani Makiyaya mazauna yankin Kudu maso-gabas a Kudancin kasar nan, Malam Ardo Sa’idu Baso, Ardon ya bayyana cewa shi da jama’arsa suna zaune kalau da abokan zamansu a yankin.

Jagoran y ace, “Babu shakka muna da kyakkyawar alakar zamantakewa tsakanin mu Fulani makiyaya da kuma ’yan kabilar Ibo. Duk da cewa wannan matsala ta kungiyar Biyafara ta faru amma mu a nan Jihar Enugu tashin hankalin bai shafe mu ba, sai dai irin abin da ba a rasawa”.

Ya ci gaba da cewa, “Kafin irin wannan mastalar ta fara tasowa da bayan faruwarta zan iya cewa akwai zaman lafiya  awannan jihar  sama da shekaru talatin da muke tare da su.

Game da kokawa da akan yi dangane da irin barnar da makiyaya ke yi wa manoma da dabbobinsu a yankin, Ardon ya ce hakika suna samun labarin aukuwar hakan a wasu jihohi, amma cewa a nasu yankin suna bin komai cikin tsari wanda hakan yasa ake samun lumana a tsakaninsu da manoman yankin ba tare da wata hatsaniya ba.

Kazalika, jagoran Fulanin ya ce a duk lokacin da suka ga wani ya taso wanda ka iya haifar da rashin jituwa a tsakani, sukan nemi abokan zamansu ne su zauna tare su yi tattauanawa ta fahimtar juna domin samun mafita ko maslaha. Idan darna ce da dabbobi suka yi, sai a yi wa barnar kima su biya mai gona hakkinsa.

A karshe, Ardon ya yi kira ga takwarorinsa a duk inda suke da su tashi tsaye su tabbatar da adalci tare da kare hakkokin jama’arsu. Sannan su yi dukkan mai yiwuwa wajen wanzan da zaman lafiya a tsakani.

SendShareTweetShare
Previous Post

Ilimi Jigo Ne Na Yakar Talauci –Masari

Next Post

Nazarin Cikar Katsina Shekaru 30

RelatedPosts

Gwamnatin Gombe Ta Sanya Dokar Hana Fita A Garin Balanga

Gwamnatin Gombe Ta Sanya Dokar Hana Fita A Garin Balanga

by Muhammad
2 hours ago
0

Daga Khalid Idris Doya, Gwamnatin Jihar Gombe ta sanar dokar...

Ramadan: Mu Yi Addu’ar Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ga Nijeriya, Inji Bukola Saraki

Ramadan: Mu Yi Addu’ar Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ga Nijeriya, Inji Bukola Saraki

by Daurawa Daurawa
4 hours ago
0

Daga Rabi'u Ali Indabawa, Abuja Tsohon Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya,...

Ramadana: Lokaci Ne Na Komawa Ga Allah, Inji Atiku

Ramadana: Lokaci Ne Na Komawa Ga Allah, Inji Atiku

by Muhammad
8 hours ago
0

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya yi kira...

Next Post

Nazarin Cikar Katsina Shekaru 30

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version