• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Mu Karɓi Kuɗin IPMAN Ba Bare Mu Hana Su Mai – Matatar Dangote

by Yusuf Shuaibu
11 months ago
in Tattalin Arziki
0
Ba Mu Karɓi Kuɗin IPMAN Ba Bare Mu Hana Su Mai – Matatar Dangote
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matatar mai ta Dangote ta fayyace cewa ba ta karɓi wani kuɗi daga Ƙungiyar Dillalan Man Fetur Masu Zaman Kansu ta Nijeriya (IPMAN) ba domin sayen manta da aka tace.

Matatar ta ce duk da cewa ana ci gaba da tattaunawa da ƙungiyar ta IPMAN, amma abin takaici ne a ce su (Mambobin IPMAN) suna fuskantar matsalar lodin man da aka tace daga matatarmu, domin a halin yanzu ba mu da wata hulɗar kasuwanci da su. Saboda haka, ba za a iya ɗaukar alhakin duk wani kuɗin da aka yi wa wasu ƙungiyoyi ba.

Sanarwar da matatar ta fitar ta hannun Babban Jami’in Yaɗa Labarunta, Mista Anthony Chiejina ta qara da cewa, “an biya kuɗin da aka ambata ta hannun Kamfanin Mai na Nijeriya (NNPCL), ba mu ba. Haka zalika, NNPCL bai yarda ko ba mu izini mu saki man fetur ga ƙungiyar IPMAN ba.

“Muna so mu jaddada cewa za mu iya biyan buƙatun al’umma na duk wani nau’in man fetur da suka haɗa da fetur, dizal, da man jiragen sama. A halin yanzu, muna iya lodin manyan motoci 2,900 a kowace rana, haka kuma muna dakon man fetur ta ruwa. Muna ba IPMAN shawara da ta yi rajista da mu kuma ta biya kai tsaye, saboda muna da isassun albarkatun man fetur don biyan buƙatun mambobinsu.

“Bugu da ƙari kuma, muna ganin yana da kyau duk masu ruwa da tsaki su guji furta kalamai marasa tushe a kafafen yaɗa labarai, domin hakan na iya kawo cikas ga ƙoƙarin sake farfaɗo da tattalin arzikin da Mai Girma Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ke yi. Gudanar da kasuwanci ta maramtacciyar hanya ba shi da amfani kuma rashin kishin ƙasa ne.

Labarai Masu Nasaba

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

Kudaden Ajiya Na Asusun Nijeriya Ya Karu Zuwa Dala Biliyan 41

“Muna ƙarfafa duk masu ruwa da tsaki su ba da haɗin kai tare da bin shawarwarin Shugaba Tinubu, da inganta tsarin haɗin kai, maimakon shiga cikin rikice-rikicen kafofin watsa labaru da farfaganda mara amfani,” in ji Chiejina.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DangoteFeturIPMANMatatar Mai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ficewar Matasa Masu Hazaka Babbar Barazana Ce Ga Ci Gaban Nijeriya – Jega

Next Post

Minista Ya Nemi Kafafen Yaɗa Labarai Da Jajircewa Wajen Kare Dimokuraɗiyya

Related

A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

7 days ago
tallafi
Tattalin Arziki

Kudaden Ajiya Na Asusun Nijeriya Ya Karu Zuwa Dala Biliyan 41

2 weeks ago
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

2 weeks ago
Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5
Tattalin Arziki

Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

2 weeks ago
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya
Tattalin Arziki

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

3 weeks ago
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku
Tattalin Arziki

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

3 weeks ago
Next Post
Minista Ya Nemi Kafafen Yaɗa Labarai Da Jajircewa Wajen Kare Dimokuraɗiyya

Minista Ya Nemi Kafafen Yaɗa Labarai Da Jajircewa Wajen Kare Dimokuraɗiyya

LABARAI MASU NASABA

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.