• English
  • Business News
Thursday, June 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Mu Karɓi Kuɗin IPMAN Ba Bare Mu Hana Su Mai – Matatar Dangote

by Yusuf Shuaibu
7 months ago
in Tattalin Arziki
0
Ba Mu Karɓi Kuɗin IPMAN Ba Bare Mu Hana Su Mai – Matatar Dangote
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matatar mai ta Dangote ta fayyace cewa ba ta karɓi wani kuɗi daga Ƙungiyar Dillalan Man Fetur Masu Zaman Kansu ta Nijeriya (IPMAN) ba domin sayen manta da aka tace.

Matatar ta ce duk da cewa ana ci gaba da tattaunawa da ƙungiyar ta IPMAN, amma abin takaici ne a ce su (Mambobin IPMAN) suna fuskantar matsalar lodin man da aka tace daga matatarmu, domin a halin yanzu ba mu da wata hulɗar kasuwanci da su. Saboda haka, ba za a iya ɗaukar alhakin duk wani kuɗin da aka yi wa wasu ƙungiyoyi ba.

Sanarwar da matatar ta fitar ta hannun Babban Jami’in Yaɗa Labarunta, Mista Anthony Chiejina ta qara da cewa, “an biya kuɗin da aka ambata ta hannun Kamfanin Mai na Nijeriya (NNPCL), ba mu ba. Haka zalika, NNPCL bai yarda ko ba mu izini mu saki man fetur ga ƙungiyar IPMAN ba.

“Muna so mu jaddada cewa za mu iya biyan buƙatun al’umma na duk wani nau’in man fetur da suka haɗa da fetur, dizal, da man jiragen sama. A halin yanzu, muna iya lodin manyan motoci 2,900 a kowace rana, haka kuma muna dakon man fetur ta ruwa. Muna ba IPMAN shawara da ta yi rajista da mu kuma ta biya kai tsaye, saboda muna da isassun albarkatun man fetur don biyan buƙatun mambobinsu.

“Bugu da ƙari kuma, muna ganin yana da kyau duk masu ruwa da tsaki su guji furta kalamai marasa tushe a kafafen yaɗa labarai, domin hakan na iya kawo cikas ga ƙoƙarin sake farfaɗo da tattalin arzikin da Mai Girma Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ke yi. Gudanar da kasuwanci ta maramtacciyar hanya ba shi da amfani kuma rashin kishin ƙasa ne.

Labarai Masu Nasaba

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

“Muna ƙarfafa duk masu ruwa da tsaki su ba da haɗin kai tare da bin shawarwarin Shugaba Tinubu, da inganta tsarin haɗin kai, maimakon shiga cikin rikice-rikicen kafofin watsa labaru da farfaganda mara amfani,” in ji Chiejina.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DangoteFeturIPMANMatatar Mai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ficewar Matasa Masu Hazaka Babbar Barazana Ce Ga Ci Gaban Nijeriya – Jega

Next Post

Minista Ya Nemi Kafafen Yaɗa Labarai Da Jajircewa Wajen Kare Dimokuraɗiyya

Related

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

5 days ago
Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

2 weeks ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

1 month ago
Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

1 month ago
Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC

1 month ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA

1 month ago
Next Post
Minista Ya Nemi Kafafen Yaɗa Labarai Da Jajircewa Wajen Kare Dimokuraɗiyya

Minista Ya Nemi Kafafen Yaɗa Labarai Da Jajircewa Wajen Kare Dimokuraɗiyya

LABARAI MASU NASABA

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

June 4, 2025
Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

June 4, 2025
Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

June 4, 2025
Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

June 4, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

June 4, 2025
Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

June 4, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

June 4, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

June 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.