• English
  • Business News
Thursday, June 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Wanda Zai Iya Kawo Tsaiko Ga Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yanzu haka ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi na ziyara a wasu kasashen Afirka, ziyarar dake zama al’adar shekaru 34 ke nan a jere da kowane ministan harkokin wajen Sin ke fara kaiwa wasu kasashen nahiyar ziyara a duk farkon kowace shekara.

Tun bayan da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi bayani game da manufar kasar Sin ga nahiyar Afrika a Tanzania, wadda ta tsara makomar huldar kasashen Sin da Afrika a sabon zamani, wadda yanzu haka ta haifar da kawance da kulla dangantaka da yarda da juna tsakanin bangarorin biyu.

  • Xi Ya Taya Felix Antoine Tshisekedi Murnar Lashe Zaben Shugaban Jamhuriyyar Dimokuradiyyar Congo
  • Shugaban Kasar Tunisiya Ya Gana Da Wang Yi

Ita dai wannan manufa da shugaba Xi Jinping ya gabatar, yayin ziyararsa ta farko da ya kai nahiyar Afrika, a matsayinsa na shugaban kasar Sin, a shekarar 2013 ta dogaro ne bisa gaskiya da samun managartan sakamako da fahimtar juna,

Bisa wadannan tsare-tsare, kasashen Sin da Afrika sun dunkule waje guda, wajen samar da tafarkin samun ci gaba na bai daya, da nufin samar da dangantaka mai karfi da ba a taba ganin irinta ba, tsakanin kasar dake nahiyar Asia da kuma nahiyar Afrika, wadanda yawan al’ummarsu ya kai biliyan 2.5, kwatankwacin daya bisa ukun al’ummar duniya baki daya.

Bayan wadannan shekaru, ana iya ganin dimbin moriyar da aka samu bisa dangantakar dake tsakanin kasar Sin da nahiyar Afrika a fannonin da suka hada da tattalin arziki,da ilimi, da cinikayya, da kayayyakin more rayuwa, da al’adu, da fannin noma,da raya masana’antu da ma kaiwa juna ziyara a bangaren manyan jami’ai da shugabannin sassan biyu.

Labarai Masu Nasaba

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

Tarukan dandalin hadin gwiwar kasar Sin da nahiyar Afrika FOCAC, da suka gudana a wurare da lokuta daban-daban, wani gagarumin ci gaba ne ga dangantakar dake tsakanin bangarorin biyu. Wadanda ke aikewa da muhimmin sako ga al’ummomin duniya cewa, Sin da Afrika sun hada hannu don samun nasara tare.

Sai dai duk da irin wannann ci gaba da sasan biyu suka, kasashen yamma, sun sha yiwa wannan alaka wata mummunan mahuguwar fahimta, har ma suka neman bata wannan dangantaka ta fannoni daban-daban. Sai dai bakin alkalami ya riga ya bushe, kuma hakar su ba za ta taba cimma ruwa ba.

Sakamakon wannan hadin gwiwa, kasashen Afrika da Sin, suna kokarin hade manufofi da dabarunsu na samun ci gaba karkashin shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya” da muradun ci gaba masu dorewa na MDD da kuma ajandar raya nahiyar ta kungiyar Tarayyar Afrika da ake son cimmawa nan zuwa shekarar 2063.

Misalin abubuwa na baya-bayan nan da wasu kasashen Afirka suka amfana da shi daga alakarsu da kasar Sin sune, filayen wasan da suka hada da na Korhogo da na San Pedro, baya ga filin wasa na Alassane Ouattara da aka kaddamar da gasar wasan cin kofin kwallon kafan nahiyar Afirka na shekarar 2024, a kasar Code D/Ivoire da kamfanin kasar Sin ya gina.

Bayanai na nuna cewa, bisa ga tsarin dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka, kawo yanzu kamfanonin kasar Sin sun gina layukan dogo a Afirka da tsawonsu ya zarce kilomita dubu 10, baya ga hanyoyin mota da suka kai kusan kilomita dubu 100, da gadoji kusan dubu da tashoshin jiragen ruwa kusan dari, da ma dimbin asibitoci da makarantu da filayen wasa.

Masana na ganin cewa, irin wadannan ayyuka za su inganta da ma saukaka harkokin zirga-zirga, baya ga kara samar da kudaden shiga, matakin da zai kara inganta rayuwar mazauna wuraren. Wannan na kara tabbatar da cewa, kasashen Sin da Afirka na kara zama tsintsiya madaurinki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaTaipeiTaiwan
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Jaddada Matsayin Najeriya Na Goyon Bayan Manufar Kasancewar Kasar Sin Daya Tak A Duniya

Next Post

Ali Nuhu Da Murja Kunya Na Cikin Mutane 150 Ma Fi Tasiri A Intanet A 2023

Related

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai
Daga Birnin Sin

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

18 hours ago
Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

19 hours ago
Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba
Daga Birnin Sin

Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

20 hours ago
Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana
Daga Birnin Sin

Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

22 hours ago
Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 
Daga Birnin Sin

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

23 hours ago
Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

1 day ago
Next Post
Murja

Ali Nuhu Da Murja Kunya Na Cikin Mutane 150 Ma Fi Tasiri A Intanet A 2023

LABARAI MASU NASABA

Hukumar kashe gobara

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

June 5, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

June 5, 2025
Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

June 5, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

June 5, 2025
Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

June 5, 2025
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

June 5, 2025
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

June 5, 2025
Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

June 5, 2025
Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

June 5, 2025
Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Muhammadu Iliyasu Bashir A Matsayin Sarkin Gwandu

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Muhammadu Iliyasu Bashir A Matsayin Sarkin Gwandu

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.