ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Kasar Tunisiya Ya Gana Da Wang Yi

by CGTN Hausa
2 years ago
Wang yi

Jiya Litinin, shugaban kasar Tunisiya Kais Saied ya gana da mamban ofishin siyasa na kwamitin tsakiyar Jam’iyyar Kwaminis ta Kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar Wang Yi a birnin Tunis, fadar mulkin kasar Tunisiya.

Da farko, Kais Saied ya bukaci Wang Yi da ya mika sakon gaisuwarsa ga shugaba Xi Jinping, yana mai cewa, ya amince da ra’ayoyin da shugaba Xi ya gabatar game da tafiyar da harkokin kasa, ya kuma yaba wa kasar Sin dangane da babbar nasarar da ta cimma a fannin zamanintar da kasar, haka kuma, ya yaba matuka kan sakamakon da aka cimma cikin shekaru 60 da suka gabata, bisa hadin gwiwa da bunkasuwar dangantaka a tsakanin kasashen biyu. Ya ce, ko da yake, akwai nisa a tsakanin kasar Sin da kasar Tunisiya, amma jama’ar kasashen biyu suna da zumunci mai zurfi a tsakaninsu, kuma kasarsa tana godiya ga kasar Sin bisa goyon bayan da ta dade tana nuna mata, lamarin da ya taimaka wajen raya kasar da kyautata zaman rayuwar al’umma. Ya ce a nan gaba kuma, kasar Tunisiya za ta ci gaba da goyon bayan shawarar “Ziri daya da hanya daya”, da koyon fasahohin kasar Sin wajen zamanintar da kasar Tunisiya bisa yanayin da take ciki. Haka kuma, kasar Tunisiya tana tsayawa tsayin daka wajen martaba manufar “kasar Sin kasa daya tak”, da kuma kudurin MDD mai lamba 2758, domin goyon bayan kasar Sin wajen kula da harkokin kasarta.

  • Kasar Sin Tana Da Cikakken Karfin Harhada Da Kera Jiragen Ruwa
  • Sin Ta Riga Ta Bayar Da Gudunmawar Da Ake Bukata Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

A nasa bangare, Wang Yi ya mika sakon gaisuwar shugaban kasar Sin Xi Jinping ga shugaba Saied, ya ce, tun bayan kulla huldar diflomasiyya a tsakanin kasar Sin da kasar Tunisiya shekaru 60 da suka gabata, dangantakar dake tsakanin kasashen biyu ta bunkasa yadda ya kamata. Kuma, abu mafi muhimmanci shi ne, bangarori biyu suna girmama juna, da nunawa juna adalci, da karfafa fahimtar juna a tsakaninsu, da kuma habaka hadin gwiwarsu, domin cimma moriyar juna. Kwanan baya, shugabannin kasashen biyu sun zanta ta wayar tarho, inda suka kara daidaita hanyar raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu. Kasar Sin tana godiya ga kasar Tunisiya, domin irin goyon bayan da ta nuna wa kasar Sin kan manyan batutuwan dake shafar ‘yancin kan kasar Sin, a sa’i daya kuma, kasar Sin tana goyon bayan kasar Tunisiya, wajen kare mulkin kai da ‘yancin kanta, da kuma kiyaye mutuncin al’ummar kasarta, kana, kasar Sin tana goyon bayan kasar Tunisiya wajen neman hanyar bunkasuwa bisa halin da take ciki, da aiwatar da gyare-gyaren raya kasa cikin ‘yanci.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, shugaba Saied da minista Wang Yi, sun yi musayar ra’ayoyi kan rikicin Isra’ila da Falesdinu.

A wannan rana, Wang Yi ya kuma gana da takwaransa na kasar Tunisiya Nabil Ammar a birnin Tunisiya.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Wang Yi ya ce, kasar Sin a shirye take ta yi mu’amala da kasar Tunisiya wajen inganta fasahohin gudanawar harkokin kasa, kuma tana goyon bayan kasar Tunisiya wajen kara karfinta na neman bunkasuwa cikin ‘yancin kai, domin samun ci gaba da wadata cikin hadin gwiwa.

A nasa bangare kuma, minista Ammar ya ce, kasarsa tana mai da matukar hankali wajen zurfafa zumuncin dake tsakanin kasashen biyu, kuma, tana godiya ga kasar Sin dangane da taimako da goyon bayan da ta nuna mata. Kasar Tunisiya tana fatan yin hadin gwiwa da kasar Sin wajen inganta dangantakar dake tsakanin kasashen biyu zuwa wani sabon matsayi. (Mai Fassarawa: Maryam Yang)

 

Wang yi
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Yanzu-yanzu: Wani Abu Ya Fashe A Tashar Iskar Gas A Ibadan

Yanzu-yanzu: Wani Abu Ya Fashe A Tashar Iskar Gas A Ibadan

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.