ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Kasar Tunisiya Ya Gana Da Wang Yi

by CGTN Hausa
2 years ago
Wang yi

Jiya Litinin, shugaban kasar Tunisiya Kais Saied ya gana da mamban ofishin siyasa na kwamitin tsakiyar Jam’iyyar Kwaminis ta Kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar Wang Yi a birnin Tunis, fadar mulkin kasar Tunisiya.

Da farko, Kais Saied ya bukaci Wang Yi da ya mika sakon gaisuwarsa ga shugaba Xi Jinping, yana mai cewa, ya amince da ra’ayoyin da shugaba Xi ya gabatar game da tafiyar da harkokin kasa, ya kuma yaba wa kasar Sin dangane da babbar nasarar da ta cimma a fannin zamanintar da kasar, haka kuma, ya yaba matuka kan sakamakon da aka cimma cikin shekaru 60 da suka gabata, bisa hadin gwiwa da bunkasuwar dangantaka a tsakanin kasashen biyu. Ya ce, ko da yake, akwai nisa a tsakanin kasar Sin da kasar Tunisiya, amma jama’ar kasashen biyu suna da zumunci mai zurfi a tsakaninsu, kuma kasarsa tana godiya ga kasar Sin bisa goyon bayan da ta dade tana nuna mata, lamarin da ya taimaka wajen raya kasar da kyautata zaman rayuwar al’umma. Ya ce a nan gaba kuma, kasar Tunisiya za ta ci gaba da goyon bayan shawarar “Ziri daya da hanya daya”, da koyon fasahohin kasar Sin wajen zamanintar da kasar Tunisiya bisa yanayin da take ciki. Haka kuma, kasar Tunisiya tana tsayawa tsayin daka wajen martaba manufar “kasar Sin kasa daya tak”, da kuma kudurin MDD mai lamba 2758, domin goyon bayan kasar Sin wajen kula da harkokin kasarta.

  • Kasar Sin Tana Da Cikakken Karfin Harhada Da Kera Jiragen Ruwa
  • Sin Ta Riga Ta Bayar Da Gudunmawar Da Ake Bukata Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

A nasa bangare, Wang Yi ya mika sakon gaisuwar shugaban kasar Sin Xi Jinping ga shugaba Saied, ya ce, tun bayan kulla huldar diflomasiyya a tsakanin kasar Sin da kasar Tunisiya shekaru 60 da suka gabata, dangantakar dake tsakanin kasashen biyu ta bunkasa yadda ya kamata. Kuma, abu mafi muhimmanci shi ne, bangarori biyu suna girmama juna, da nunawa juna adalci, da karfafa fahimtar juna a tsakaninsu, da kuma habaka hadin gwiwarsu, domin cimma moriyar juna. Kwanan baya, shugabannin kasashen biyu sun zanta ta wayar tarho, inda suka kara daidaita hanyar raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu. Kasar Sin tana godiya ga kasar Tunisiya, domin irin goyon bayan da ta nuna wa kasar Sin kan manyan batutuwan dake shafar ‘yancin kan kasar Sin, a sa’i daya kuma, kasar Sin tana goyon bayan kasar Tunisiya, wajen kare mulkin kai da ‘yancin kanta, da kuma kiyaye mutuncin al’ummar kasarta, kana, kasar Sin tana goyon bayan kasar Tunisiya wajen neman hanyar bunkasuwa bisa halin da take ciki, da aiwatar da gyare-gyaren raya kasa cikin ‘yanci.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, shugaba Saied da minista Wang Yi, sun yi musayar ra’ayoyi kan rikicin Isra’ila da Falesdinu.

A wannan rana, Wang Yi ya kuma gana da takwaransa na kasar Tunisiya Nabil Ammar a birnin Tunisiya.

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Wang Yi ya ce, kasar Sin a shirye take ta yi mu’amala da kasar Tunisiya wajen inganta fasahohin gudanawar harkokin kasa, kuma tana goyon bayan kasar Tunisiya wajen kara karfinta na neman bunkasuwa cikin ‘yancin kai, domin samun ci gaba da wadata cikin hadin gwiwa.

A nasa bangare kuma, minista Ammar ya ce, kasarsa tana mai da matukar hankali wajen zurfafa zumuncin dake tsakanin kasashen biyu, kuma, tana godiya ga kasar Sin dangane da taimako da goyon bayan da ta nuna mata. Kasar Tunisiya tana fatan yin hadin gwiwa da kasar Sin wajen inganta dangantakar dake tsakanin kasashen biyu zuwa wani sabon matsayi. (Mai Fassarawa: Maryam Yang)

 

Wang yi
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

MASU ALAKA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
Daga Birnin Sin

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Daga Birnin Sin

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Next Post
Yanzu-yanzu: Wani Abu Ya Fashe A Tashar Iskar Gas A Ibadan

Yanzu-yanzu: Wani Abu Ya Fashe A Tashar Iskar Gas A Ibadan

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.