• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Za Mu Bari NNPP Ta Yi Magudin Zabe A Kano Ba —Gwamnatin Kano

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Ba Za Mu Bari NNPP Ta Yi Magudin Zabe A Kano Ba —Gwamnatin Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Kano karkashin jam’iyyar APC ta sha alwashin tabbatar da hana duk wani yunkuri da ‘yan adawa za su yi na yin magudi a zaben gwamnoni da na ‘yan majalisar jiha da za a gudanar a jihar a ranar 11 ga watan Maris.

Gwamnatin ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida na jihar, Malam Muhammad Garba, ya fitar ranar Litinin a Kano.

  • An Fara Bincike Kan Sojan Da Ya Kashe Abokin Aikinsa, Ya Kuma Hallaka Kansa A Sakkwato 
  • Kotun Koli Ta Tabbatar Lawal Dare A Matsayin Dan Takarar Gwamnan PDP A Zamfara 

Ya ce dole ne gwamnati ta jawo hankalin jama’a “saboda hakan na iya kawo cikas ga zaben gwamna da na ‘yan majalisun da za a yi.

Ya kuma kara da cewa gwamnati ta samu sahihin bayanai kan yadda za a dauki ‘yan baranda daga kauyukan Kano da wajenta domin tada zaune tsaye a zaben ta hanyar tashin hankali, magudin zabe, kwace akwatuna da kone-kone.

Garba ya kara da cewa, a shekarar 2019 ‘yan adawa sun gudanar da wani shiri na magudin zabe, musamman a kananan hukumomi, inda matasa, wadanda galibi ba su da katin zabe, suka daura damarar yin aika-aika.

Labarai Masu Nasaba

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

Kwamishinan ya yi zargin cewa a wannan karon ‘yan adawa na shirin kawo hargitsi ta hanyar amfani da ‘yan baranda don tayar da tarzoma da nufin tarwatsa masu kada kuri’a a rumfunan zabe domin samun damar yin magudin zabe da kuma karkatar da ra’ayin jama’a.

Ya kuma yi zargin cewa sanarwar da ‘yan adawa a jihar suka fitar wasa ne kawai amma sun kammala munanan shirye-shiryensu na ganin sun kawo cikas a harkar zabe tare da tayar da tarzoma.

Sai dai Garba ya ba da tabbacin cewa gwamnatin APC za ta tabbatar da cewa an samu zaman lafiya a jihar.

Kwamishinan ya yi kira ga jami’an tsaro da abin ya shafa da su kasance cikin shiri don sauke nauyin da ya rataya a wuyansu ta hanyar kama duk wani mutum ko wata kungiya da ke da niyyar tayar da fitina don hana mutane yin amfani da ikonsu.

Leadership Hausa ya rawaito cewa babbar jam’iyyar adawa ta NNPP a jihar, a ranar Litinin ta sanar da mazauna jihar ta hanyar wani taron manema labarai kan shirin da jam’iyyar APC mai mulki ta yi na murza tsarin dimokuradiyya ta hanyar tsoratar da masu zabe.

Don haka jam’iyyar New NNPP ta bukaci hukumomin tsaro da su samar da zaben gwamna da na ‘yan majalisar jiha cikin kwanciyar hankali da lumana ba tare da tashin hankali ba.

Wani jigo a jam’iyyar, Dokta Bappa Bichi, ya shaida wa manema labarai cewa, muradin ‘yan Nijeriya na zaben shugabannin da suke so ba zai yiwu ba idan hukumomin tsaro suka kasa samar da daidaito ga dukkanin jam’iyyun siyasa.

A cewarsa, hakan zai ba da damar gudanar da zabe na gaskiya da adalci.

Bichi ya kuma bukaci Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) da hukumomin tsaro da su kasance a tsaka-tsaki da adalci da kuma rashin nuna banbanci wajen gudanar da ayyukansu a lokutan zabe da kuma bayan zabe.

A baya dai rundunar ‘yansandan jihar ta gargadi jam’iyyun siyasa da ‘yan takararsu da magoya bayansu kan duk wani tashin hankali.

Kakakin rundunar ‘yansandan jihar, SP Abdullahi Kiyawa, ya kuma bayar da tabbacin ba za su dauki bangare a zaben ba.

A cewarsa, hukumomin tsaro sun kuduri aniyar tabbatar da an gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali da kama tare da hukunta wadanda suka tada tarzoma kamar yadda aka yi a lokacin zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCGwamnatin KanoJam'iyyaMagudiNNPPSiyasaTsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Fara Bincike Kan Sojan Da Ya Kashe Abokin Aikinsa, Ya Kuma Hallaka Kansa A Sakkwato 

Next Post

Ka Daina Gararamba A Titi Ka Tafi Kotu —Martanin APC Ga Atiku

Related

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa
Labarai

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

37 minutes ago
DSS
Labarai

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

3 hours ago
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

4 hours ago
katsina
Labarai

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

5 hours ago
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno
Manyan Labarai

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

7 hours ago
Sanusi
Manyan Labarai

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

18 hours ago
Next Post
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Ka Daina Gararamba A Titi Ka Tafi Kotu —Martanin APC Ga Atiku

LABARAI MASU NASABA

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

June 4, 2025
DSS

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

June 4, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 4, 2025
katsina

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

June 4, 2025
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

June 4, 2025
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

June 3, 2025
Sanusi

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.