ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotun Koli Ta Tabbatar Lawal Dare A Matsayin Dan Takarar Gwamnan PDP A Zamfara 

by Sadiq
3 years ago
Kotun Koli

Kotun kolin ta tabbatar da Dauda Lawal Dare a matsayin dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a Jihar Zamfara a zaben gwamnan jihar da za a yi ranar 11 ga watan Maris.

Alkalin kotun mai shari’a Adamu Jauro ne ya jagoranci, kwamitin alkalai biyar, ya yi watsi da karar da wani dan takarar gwamna, Dakta Ibrahim Gusau ya shigar kan zaben.

  • Sin Na Ci Gaba Da Dukufa Kan Bude Kofa Ga Ketare
  • Wani Soja Ya Hallaka Kwamandansa Ya Kuma Bindige Kansa Da Wasu Sojoji 2 A Sokoto

Ta tabbatar da abin da Mista Damian Dodo SAN, lauya ga Lawal Dare ya gabatar cewa an gabatar da wanda yake karewa bisa doka.

ADVERTISEMENT

Jauro ya amince da hukuncin kotun daukaka kara da ta amince da zaben fidda gwani na biyu da ya samar da dan takarar.

A zaben fidda gwanin dai Lawal Dare ya samu kuri’u 442 inda ya samu nasara a kan Gusau da sauran ‘yan takara.

LABARAI MASU NASABA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

Jauro ya ce wata babbar kotun tarayya da ke Gusau wadda ta soke zaben fidda gwani har sau biyu ba ta da hurumi a lokacin da ta yanke hukunci kan karar da Gusau ya shigar.

Zaben fidda gwani na gwamnan PDP na farko da aka gudanar a ranar 25 ga Mayu, 2022 an kalubalanci shi a wata babbar kotun tarayya da ke Gusau kuma ta soke shi.

A hukuncin da babbar kotun ta yanke ta bayar da umarnin sake gudanar da sabon zaben fidda gwani da aka gudanar a ranar 23 ga Satumba, 2022 amma kuma kotun ta soke shi saboda wasu kurakurai.

Bai gamsu da hukuncin babbar kotun ba, Dauda Lawal-Dare, Adamu Maina-Waziri, shugaban kwamitin zaben fidda gwani; sannan Kanar Bala Mande mai ritaya ya garzaya kotun daukaka kara domin neman tazarce.

Wadanda suka amsa karar sun hada da Dakta Ibrahim Shehu-Gusau, Alhaji Wadatau Madawaki, Hafiz Nuhuche da kuma Hukumar Zabe mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC).

A cikin hukuncin da aka yanke wanda mai shari’a Abubakar Talba a madadin wasu ya karanta, kotun daukaka kara ta ce wadanda suka shigar da kara sun yi nasarar tabbatar da dukkanin wasu dalilai guda bakwai na daukaka kara da lauyoyinsu suka yi masa, kuma kotun ta yanke hukuncin ga abin da ya dace.

Talba ya yi watsi da duk wani yunkuri na farko kan cancantar karar bisa tanadin shari’a da kuma sha’awar sauraren shari’a, yana mai cewa gazawar fasaha ba za ta iya maye gurbin tanadin shari’a ba.

Ya ce alkalin babbar kotun ya yi kuskure kan takardun rangwamen da INEC ta gabatar kuma kotun ba ta ayyana lokacin sake gudanar da zabe da kuma sanarwar shiga zabe ba.

MASU ALAKA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Next Post
Jam’iyyar NNPP Ta Bukaci Jami’an Tsaro Su Tabbatar An Yi Sahihin Zabe A Kano

Jam'iyyar NNPP Ta Bukaci Jami'an Tsaro Su Tabbatar An Yi Sahihin Zabe A Kano

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.