• English
  • Business News
Sunday, June 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babbar Matsalar Da Ta Kamata APC Ta Magance – Gwamna Sule

by Zubairu M Lawal
3 years ago
in Labarai
0
Babbar Matsalar Da Ta Kamata APC Ta Magance – Gwamna Sule
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Zubairu M Lawal

Gwamnan Jihar Nasarawa, Injiniya Abdullahi Sule ya yi kira ga kwamitin gudanarwa na jam’iyyar APC mai mulki da su yi amfani da lokacin gabanin zaben 2023, don kawar da matsalolin da suka dabaibaye jam’iyyar APC.

Gwamnan ya ce a yi kokari a hada kai a samu sulhu da kuma kwantar da hankulan ‘ya’yan jam’iyyar, musamman abin da ya faru bayan zaben fid da gwani.

  • Halin Da Ake Ciki A ‘Yandoton Daji Bayan Nadin Sarautar Dan Ta’adda

Injiniya Sule ya yi wannan kiran ne a lokacin da ya karbi bakoncin shugaban jam’iyyar APC na kasa, Sanata Abdullahi Adamu, yayin da ya kai ziyarar gaisuwar Sallah da ta’aziyya a fadar gwamnatin da ke Lafiya a ranar Asabar.

A cewar gwamnan, ya zama wajibi jam’iyyar APC ta shiga zaben 2023 a dunkule cikin hadin kan ‘ya’yanta tare da zaman lafiya.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

Ya kuma yi kira ga shugaban jam’iyyar APC na kasa da ya yi amfani da kwarewarsa wajen kawar da tashin hankalin da ke kara ta’azzara a cikin jam’iyyar.

Ya ce, saboda abubuwan da suka faru a sakamakon zaben fid da gwani na jam’iyyar APC da aka kammala kwanan nan, lamarin da ya sanya wasu ‘ya’yan jam’iyyar suka rika ficewa daga APC zuwa wasu jam’iyyun. Ya ce, da dama membobin jam’iyyar APC masu rike da mukamai sun fice daga jam’iyyar saboda da zargin rashin adalci da aka yi masu a lokacin zaben. Gwamnan ya ce lamarin ya shafi ko’ina cikin fadin kasar nan.

“Kusan watanni takwas kafin zabe, wannan ya rage gare mu musamman tsofaffin ‘yan siyasa irin ku, mu yi amfani da damarmu wajen kwantar da hankula da duk wadanda suka ji rauni. Mu kuma janyosu su dawo cikinmu hakan shi ne damarmu na samun nasara.

” Ya zama wajibi mu yi duk mai yuhuwa wajen ganawa da sauran ‘ya’yan jam’iyyar domin sulhuntawa”.

Hakazalika, gwamnan ya yi kira ga masu taimaka wa shugaban jam’iyyar na kasa, su ma su yi amfani da wannan damar wajen tuntubar ‘ya’yan jam’iyyar dan jin ra’ayinsu da kuma kauce wa al’amuran da ka iya haifar da matsala ga jam’iyyar nan gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Muna Da Irin Akidar NEPU Da PRP A Siyasarmu -Shugaban SDP

Next Post

Cikin Watanni Uku An Haifi Yara Sama Da 27,000 A Kano

Related

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah
Ilimi

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

17 minutes ago
bakin wake
Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

2 hours ago
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar
Labarai

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

5 hours ago
Gwamnan kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

6 hours ago
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina
Labarai

Majalisar Dokokin Katsina Ta Ayyana Gwamna Radda A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A 2027

6 hours ago
An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya
Labarai

An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

7 hours ago
Next Post
Cikin Watanni Uku An Haifi Yara Sama Da 27,000 A Kano

Cikin Watanni Uku An Haifi Yara Sama Da 27,000 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

June 1, 2025
bakin wake

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

June 1, 2025
‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

June 1, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

June 1, 2025
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

June 1, 2025
Gwamnan kano

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

June 1, 2025
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Majalisar Dokokin Katsina Ta Ayyana Gwamna Radda A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A 2027

June 1, 2025
An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

June 1, 2025
Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

June 1, 2025
Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Shirin Aure Tun Kafin Lokacin Ya Zo

Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Shirin Aure Tun Kafin Lokacin Ya Zo

June 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.