ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
11 months ago
Matatar dangote

Kungiyar Tuntuɓa ta Arewacin Nijeriya, wato Arewa Consultative Forum (ACF), ta yi magana da kakkausan harshe kan abin da ta kira yunkurin da ake ta yi na kawo cikas ga harkokin Matatar Man Dangote da Kamfanin Sinadarai na Petrochemicals da ke Ibeju-Lekki, Legas.

 

ACF ta nuna damuwa kan abin da ta bayyana a matsayin “makirci da aka boye” da ke nufin lalata mafi girman matatar man cikin gida mallakar ’yan Nijeriya.

ADVERTISEMENT
  • ‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar
  • Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

A cikin wata sanarwa da Sakatarenta na Yada Labarainta na Kasa, Farfesa T. A. Muhammad-Baba, ya fitar, Arewa Consultatibe Forum (ACF) ta bayyana damuwa kan irin jerin matsalolin da suka rika hana ci gaban Matatar Man Dangote tun daga kafuwarta har zuwa matakin aikinta na yanzu.

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

A cewar kungiyar, wadannan kalubalen sun hada da takurawar dokoki daga hukumomin gwamnati, karancin isar da danyen mai daga Kamfanin Man Kasa na Nijeriya (NNPC), matsalolin da suka shafi farashin kayayyaki, da kuma tsoma bakin kungiyoyin ma’aikata da na dillalan man fetur.

 

ACF ta fi mayar da hankali ne kan rawar da Kungiyar ’Yan Kasuwar Man Fetur ta Nijeriya (IPMAN), Kungiyar Ma’aikatan Man Fetur da Iskar Gas ta Nijeriya (NUPENG), da Kungiyar Manyan Ma’aikatan Man Fetur da Iskar Gas ta Nijeriya (PENGASSAN) suka taka, tana zarginsu da shiga cikin ayyukan tada hankali, ciki har da zanga-zanga da barazana, wadanda suka kara dagula harkokin aiki na matatar man.

“Yanzu abin yana kara bayyana a fili cewa akwai wasu boyayyun kungiyoyi da ke da niyyar ganin wannan babbar masana’antar cikin gida ta gaza,” in ji sanarwar. “Wannan yana nuna irin tsarin makirci daya da ya sa matatun man gwamnati guda hudu na Nijeriya suka gaza aiki yadda ya kamata.”

ACF ta nuna goyon baya ga matakin da Kamfanin Dangote Group ya dauka na neman kariya ta shari’a domin tabbatar da ci gaban ayyukansa, tare da zargin kungiyar PENGASSAN da karya umarnin kotu da ke hana ta kawo cikas ga ayyukan matatar man.

Kungiyar ta bayyana wannan ketare iyaka a matsayin raini kai tsaye ga tsarin shari’a na Nijeriya da kuma misali mai hadari ga dangantakar masana’antu a kasar.

Kungiyar ta kuma nuna goyon baya ga ra’ayoyin da Sanata Adams Oshiomhole da Sanata Mohammed Ali Ndume suka bayyana kwanan nan, inda suka ba da shawarar cewa a bai wa matatar man damar ta daidaita harkokinta kafin a kawo batun kungiyoyin kwadago a cikinta.

A cewar ACF, “ba za ka iya sanya kungiyar kwadago a wurin aiki da har yanzu yana cikin matakin farko na fara aiki ba.”

Bugu da kari, ACF ta yi kira da a kafa kwamitin binciken shari’a domin gudanar da cikakken bincike kan yawan yajin aikin da ake ta yi wanda ke nufin manyan cibiyoyi na gwamnati da masu zaman kansu. Ta ce wannan mataki zai taimaka wajen gano mutanen da ke bayan abin da ta bayyana a matsayin shiryayyen kamfen na hana ci gaban masana’antu a Nijeriya.

Saboda haka, kungiyar ta shawarci kungiyoyin kwadago da su guji duk wani aiki da zai iya kawo cikas ga kokarin zuba jari na cikin gida.

Dangote
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Dangote
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Dangote

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun 'Yancin Kai

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.