ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
9 months ago
Matatar dangote

Kungiyar Tuntuɓa ta Arewacin Nijeriya, wato Arewa Consultative Forum (ACF), ta yi magana da kakkausan harshe kan abin da ta kira yunkurin da ake ta yi na kawo cikas ga harkokin Matatar Man Dangote da Kamfanin Sinadarai na Petrochemicals da ke Ibeju-Lekki, Legas.

 

ACF ta nuna damuwa kan abin da ta bayyana a matsayin “makirci da aka boye” da ke nufin lalata mafi girman matatar man cikin gida mallakar ’yan Nijeriya.

ADVERTISEMENT
  • ‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar
  • Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

A cikin wata sanarwa da Sakatarenta na Yada Labarainta na Kasa, Farfesa T. A. Muhammad-Baba, ya fitar, Arewa Consultatibe Forum (ACF) ta bayyana damuwa kan irin jerin matsalolin da suka rika hana ci gaban Matatar Man Dangote tun daga kafuwarta har zuwa matakin aikinta na yanzu.

 

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

A cewar kungiyar, wadannan kalubalen sun hada da takurawar dokoki daga hukumomin gwamnati, karancin isar da danyen mai daga Kamfanin Man Kasa na Nijeriya (NNPC), matsalolin da suka shafi farashin kayayyaki, da kuma tsoma bakin kungiyoyin ma’aikata da na dillalan man fetur.

 

ACF ta fi mayar da hankali ne kan rawar da Kungiyar ’Yan Kasuwar Man Fetur ta Nijeriya (IPMAN), Kungiyar Ma’aikatan Man Fetur da Iskar Gas ta Nijeriya (NUPENG), da Kungiyar Manyan Ma’aikatan Man Fetur da Iskar Gas ta Nijeriya (PENGASSAN) suka taka, tana zarginsu da shiga cikin ayyukan tada hankali, ciki har da zanga-zanga da barazana, wadanda suka kara dagula harkokin aiki na matatar man.

“Yanzu abin yana kara bayyana a fili cewa akwai wasu boyayyun kungiyoyi da ke da niyyar ganin wannan babbar masana’antar cikin gida ta gaza,” in ji sanarwar. “Wannan yana nuna irin tsarin makirci daya da ya sa matatun man gwamnati guda hudu na Nijeriya suka gaza aiki yadda ya kamata.”

ACF ta nuna goyon baya ga matakin da Kamfanin Dangote Group ya dauka na neman kariya ta shari’a domin tabbatar da ci gaban ayyukansa, tare da zargin kungiyar PENGASSAN da karya umarnin kotu da ke hana ta kawo cikas ga ayyukan matatar man.

Kungiyar ta bayyana wannan ketare iyaka a matsayin raini kai tsaye ga tsarin shari’a na Nijeriya da kuma misali mai hadari ga dangantakar masana’antu a kasar.

Kungiyar ta kuma nuna goyon baya ga ra’ayoyin da Sanata Adams Oshiomhole da Sanata Mohammed Ali Ndume suka bayyana kwanan nan, inda suka ba da shawarar cewa a bai wa matatar man damar ta daidaita harkokinta kafin a kawo batun kungiyoyin kwadago a cikinta.

A cewar ACF, “ba za ka iya sanya kungiyar kwadago a wurin aiki da har yanzu yana cikin matakin farko na fara aiki ba.”

Bugu da kari, ACF ta yi kira da a kafa kwamitin binciken shari’a domin gudanar da cikakken bincike kan yawan yajin aikin da ake ta yi wanda ke nufin manyan cibiyoyi na gwamnati da masu zaman kansu. Ta ce wannan mataki zai taimaka wajen gano mutanen da ke bayan abin da ta bayyana a matsayin shiryayyen kamfen na hana ci gaban masana’antu a Nijeriya.

Saboda haka, kungiyar ta shawarci kungiyoyin kwadago da su guji duk wani aiki da zai iya kawo cikas ga kokarin zuba jari na cikin gida.

Dangote
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
  • Sulaiman
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
  • Sulaiman
    Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
  • Sulaiman
    Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci
Dangote
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Next Post
Dangote

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun 'Yancin Kai

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.