ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
9 months ago
Nnaji

Ministan Kirkire-kirkire, Kimiyya da Fasaha, Geoffrey Uche Nnaji, ya yi murabus daga majalisar ministocin Shugaba Bola Ahmed Tinubu sakamakon zargin jabun takardar shaida da aka yi masa.

 

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin bayani da dabarun sadarwa, Bayo Onanuga, ya tabbatar da murabus din a cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Litinin, inda ya bayyana cewa Shugaban Kasa ya amince da murabus din “cikin natsuwa da sadin rai.”

ADVERTISEMENT
  • Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025
  • Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Dambarwar Nnaji ta fara ne bayan kafar labarai ta Premium Times ta wallafa sakamakon binciken da ta gudanar game da zargin jabun takardar shaidar karatun Nnaji.

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

Wata kafar labarai daban, Peoples Gazette, tun da farko a shekarar 2024, ta ruwaito labaran da ke zarginsa da yin jabun takardar shaidar NYSC.

 

Sai dai Nnaji ya karyata labarin da Premium Times ta wallafa, yana mai cewa zargin aiki ne na abokan hamayyar siyasa a Jiharsa ta Enugu.

 

Tsohon ministan, wanda aka nada a watan Agusta 2023, ya mika takardar murabus dinsa a ranar Litinin ga Shugaban Kasa, inda ya nuna godiyarsa kan damar da aka ba shi ta yi wa kasa hidima.

 

A cikin wasikar tasa, tsohon ministan ya bayyana cewa ya zama abin kai hare-hare na “tsananin batanci” daga abokan hamayyar siyasa da ke neman bata masa suna.

 

“Ina gode wa Shugaban Kasa bisa amincewa da ni da kuma damar da ya ba ni na bayar da gudunmawa ga ci gaban kasa,” in ji Nnaji, yana mai kara da cewa yana janyewa ne don kare mutuncin gwamnatin.

 

Shugaba Tinubu, yayin da ya amince da murabus dinsa, ya yaba wa Nnaji bisa hidimar da ya bayar ga kasa tare da yi masa fatan alheri a harkokinsa na gaba.

 

Jaridar LEADERSHIP ta ruwaito cewa matsin lamba na karuwa kan ministan bayan da jami’ar Unibersity of Nigeria, Nsukka (UNN) ta nesanta kanta daga takardar shaidar da ake zargin Nnaji ya gabatar.

 

A cikin wata wasika mai dauke da kwanan wata 2 ga Oktoba, 2025, wadda Mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfa Simon Ortuanya, ya sanya wa hannu, jami’ar ta bayyana cewa bayanan da ke hannunta sun nuna cewa Nnaji, mai lambar shigar makaranta 1981/30725, an karbe shi a shekarar 1981 domin karatun Microbiology/Biochemistry, amma bai kammala karatunsa ba.

“Saboda haka, Jami’ar Nijeriya, Nsukka ba ta taba bayar da takardar shaidar da ake ikirari a watan Yuli 1985 ga Mista Geoffrey Uchechukwu Nnaji ba, kuma ba za ta iya bayar da ita ba,” in ji jami’ar.

Jami’ar ta ce wannan matsayi nata ya yi daidai da abin da ta bayyana a cikin wata wasika da ta aike wa Hukumar Karbar Korafe-korafe ta Jama’a a ranar 13 ga Mayu, 2025, a matsayin amsa ga irin wannan tambaya da aka yi a baya.

Sai dai a cikin takardarsa da ya gabatar gaban kotu, Nnaji ya amince cewa har yanzu bai karbi takardar shaidar digirinsa daga jami’ar ba, inda ya danganta jinkirin da abin ya samu ga abin da ya kira “rashin hadin kai” daga jami’an UNN.

Fadar Shugaban Kasa ta bayyana cewa ba za ta dauki mataki kan lamarin ba saboda shari’ar tana gaban kotu.

Sai dai, Cif Uche Nnaji ya riga ya karyata zargin jabun takardar shaidar karatu da aka yi masa, inda ya nemi hukumar jami’ar da ta saki takardar shaidar karatunsa.

A yayin taron manema labarai da aka gudanar a Abuja a ranar Litinin, ministan ya bayyana cewa zargin jabun takarda na da tushe na siyasa, kuma an tsara shi ne da nufin bata masa suna kafin zaben gwamna na 2027 a jiharsa.

A halin yanzu, Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta tsara ranar 10 ga Nuwamba domin sauraron karar da Minista Nnaji ya shigar kan Jami’ar UNN.

Ministan ya shigar da karar mai lamba FHC/ABJ/CS/1909/2025 ne sakamakon zargin jabun takardar shaida da aka yi masa.

Nnaji
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
Nnaji
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Next Post
Matatar dangote

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.