• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Abin Da Zai Bata Sunan Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

by CMG Hausa
3 years ago

A duk lokacin da aka bullo da wata manufa ko hadin gwiwa da nufin inganta rayuwar al’ummomin kasashen duniya, ya kamata kowa ya ga sakamakon hakan a zahiri, kamar yadda shawarar “ziri daya da hanya daya” ta samarwa kasashen da ke cikinta da ma hadin gwiwar kasashen Sin da Afirka da ya haifar da gagarumin sakamakon, sabanin yadda Amurka da kawayenta ke neman bata sunan shawarar yayin taron G7 na baya-bayan da suka gudanar a kasar Jamus.

Sai dai duk wani surutu da Amurka da masu neman bata sunan shawarar za su yi, hakarsu ba za ta cimma ruwa ba, domin kan Mage ya riga ya waye, galibin kasashen da suka amfana da shawarar, ba za su taba yarda a yi musu sakiyar da babu ruwa ba.

Har kullum kasar Sin wadda ta gabatar da shawarar “ziri daya da hanya daya”, tana maraba da duk wata shawarar da za ta inganta muhimman ababen more rayuwar al’ummar duniya. A hannu guda kuma, tana nuna adawa ga duk wani yunkuri na bata sunan shawarar “ziri daya da hanya daya”, bisa hujjar inganta muhimman ababen more rayuwar al’umma, don cimma wani muradun siyasa.

Wannan batu na zuwa ne, yayin da shugaban Amurka Joe Bide a wajen taron kolin kasashen G7, ya sanar da kaddamar da wai, wani shirin hadin gwiwa kan inganta muhimman ababen more rayuwar al’umma da zuba jari a duniya”, har ma wasu manyan jami’an gwamnatin Amurka da ba’a san ko su waye ba, sun rika furta kalamai na shafawa shawarar “ziri daya da hanya daya” ta kasar Sin bakin fenti. Duniya ta sha jin surutu da alkawura daga bangaren Amurka ba tare da cikawa ba.

Wani abin takaici ma shi ne, wai kasar da ba ta wadatu da ababen more rayuwa a cikin gidan ta ba , ita ce za ta jagoranci aiwatar da abin da ake kira ayyukan samar da ababen more rayuwa a duniya. Amma idan mutum ya ce, zai ba ka riga to ka kalli ta wuyansa.

LABARAI MASU NASABA

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Idan ba a manta ba, a yayin taron G7 da aka gudanar a shekarar da ta gabata, an bijiro da maganar shawarar hadin gwiwa da ake kira “Sake gina duniya mai kyau” (B3W), tare da shirin zuba jarin sama da dalar Amurka tiriliyan 40 kan bukatun kayayyakin more rayuwa a kasashe masu tasowa. A wancan lokacin, Biden ya ce shirin zai fi dacewa da bukatun samar da ababen more rayuwa na kasashe daban-daban fiye da shirin “ziri daya da hanya daya” da kasar Sin ta gabatar.

Amma rashin tsari da neman cimma moriya ta siyasa, wancan shirin bai je ko’ina ba, saboda nuna bangaranci a Amurka. Kuma har zuwa wannan lokaci adadin kudaden da aka saka a cikin ayyukan da ke da alaka, dalar Amurka miliyan 6 ne kawai, karya fure take ba ’ya’ya”.

Sanin kowane cewa, kasashe masu tasowa suna fuskantar babban gibin kudade wajen gina ababen more rayuwa. Idan har da gaske ‘yan siyasar Amurka suna son ba da taimakon kudi, wannan abu ne mai kyau.

Amma idan har ba sa son baiwa kasashe masu tasowa gudummawa, sai neman su yi wasa da hankali ne, to duk wasu sabbin sharuddan da suka kirkira, ba za su iya yaudarar kasashen da suka amfana da fa’idar shawarar “ziri daya da hanya daya” da kasar Sin ta gabatar ba. Ruwan da ya duka ka, shi ne ruwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal
Daga Birnin Sin

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025
Daga Birnin Sin

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza
Daga Birnin Sin

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
Next Post
Yadda ‘Yan Filato Ke Rajistar Katin Zabe Duk Da Mamakon Ruwan Sama

Yadda 'Yan Filato Ke Rajistar Katin Zabe Duk Da Mamakon Ruwan Sama

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025
An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.