• English
  • Business News
Wednesday, June 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Abin Da Zai Bata Sunan Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Babu Abin Da Zai Bata Sunan Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A duk lokacin da aka bullo da wata manufa ko hadin gwiwa da nufin inganta rayuwar al’ummomin kasashen duniya, ya kamata kowa ya ga sakamakon hakan a zahiri, kamar yadda shawarar “ziri daya da hanya daya” ta samarwa kasashen da ke cikinta da ma hadin gwiwar kasashen Sin da Afirka da ya haifar da gagarumin sakamakon, sabanin yadda Amurka da kawayenta ke neman bata sunan shawarar yayin taron G7 na baya-bayan da suka gudanar a kasar Jamus.

Sai dai duk wani surutu da Amurka da masu neman bata sunan shawarar za su yi, hakarsu ba za ta cimma ruwa ba, domin kan Mage ya riga ya waye, galibin kasashen da suka amfana da shawarar, ba za su taba yarda a yi musu sakiyar da babu ruwa ba.

Har kullum kasar Sin wadda ta gabatar da shawarar “ziri daya da hanya daya”, tana maraba da duk wata shawarar da za ta inganta muhimman ababen more rayuwar al’ummar duniya. A hannu guda kuma, tana nuna adawa ga duk wani yunkuri na bata sunan shawarar “ziri daya da hanya daya”, bisa hujjar inganta muhimman ababen more rayuwar al’umma, don cimma wani muradun siyasa.

Wannan batu na zuwa ne, yayin da shugaban Amurka Joe Bide a wajen taron kolin kasashen G7, ya sanar da kaddamar da wai, wani shirin hadin gwiwa kan inganta muhimman ababen more rayuwar al’umma da zuba jari a duniya”, har ma wasu manyan jami’an gwamnatin Amurka da ba’a san ko su waye ba, sun rika furta kalamai na shafawa shawarar “ziri daya da hanya daya” ta kasar Sin bakin fenti. Duniya ta sha jin surutu da alkawura daga bangaren Amurka ba tare da cikawa ba.

Wani abin takaici ma shi ne, wai kasar da ba ta wadatu da ababen more rayuwa a cikin gidan ta ba , ita ce za ta jagoranci aiwatar da abin da ake kira ayyukan samar da ababen more rayuwa a duniya. Amma idan mutum ya ce, zai ba ka riga to ka kalli ta wuyansa.

Labarai Masu Nasaba

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Idan ba a manta ba, a yayin taron G7 da aka gudanar a shekarar da ta gabata, an bijiro da maganar shawarar hadin gwiwa da ake kira “Sake gina duniya mai kyau” (B3W), tare da shirin zuba jarin sama da dalar Amurka tiriliyan 40 kan bukatun kayayyakin more rayuwa a kasashe masu tasowa. A wancan lokacin, Biden ya ce shirin zai fi dacewa da bukatun samar da ababen more rayuwa na kasashe daban-daban fiye da shirin “ziri daya da hanya daya” da kasar Sin ta gabatar.

Amma rashin tsari da neman cimma moriya ta siyasa, wancan shirin bai je ko’ina ba, saboda nuna bangaranci a Amurka. Kuma har zuwa wannan lokaci adadin kudaden da aka saka a cikin ayyukan da ke da alaka, dalar Amurka miliyan 6 ne kawai, karya fure take ba ’ya’ya”.

Sanin kowane cewa, kasashe masu tasowa suna fuskantar babban gibin kudade wajen gina ababen more rayuwa. Idan har da gaske ‘yan siyasar Amurka suna son ba da taimakon kudi, wannan abu ne mai kyau.

Amma idan har ba sa son baiwa kasashe masu tasowa gudummawa, sai neman su yi wasa da hankali ne, to duk wasu sabbin sharuddan da suka kirkira, ba za su iya yaudarar kasashen da suka amfana da fa’idar shawarar “ziri daya da hanya daya” da kasar Sin ta gabatar ba. Ruwan da ya duka ka, shi ne ruwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Masu Muguwar Niyya Ba Za Su Samu Biyan Bukata Ba

Next Post

Yadda ‘Yan Filato Ke Rajistar Katin Zabe Duk Da Mamakon Ruwan Sama

Related

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?
Daga Birnin Sin

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

14 hours ago
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

16 hours ago
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba
Daga Birnin Sin

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

17 hours ago
Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu
Daga Birnin Sin

Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

20 hours ago
Sabuwar Shugabar Kwamitin Wasannin Olympics Na Duniya Na Fatan Sake Ziyartar Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Sabuwar Shugabar Kwamitin Wasannin Olympics Na Duniya Na Fatan Sake Ziyartar Kasar Sin

1 day ago
Xi Jinping Zai Halarci Bikin Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan Da Yakin Kin Tafarkin Murdiya
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Zai Halarci Bikin Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan Da Yakin Kin Tafarkin Murdiya

1 day ago
Next Post
Yadda ‘Yan Filato Ke Rajistar Katin Zabe Duk Da Mamakon Ruwan Sama

Yadda 'Yan Filato Ke Rajistar Katin Zabe Duk Da Mamakon Ruwan Sama

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

June 25, 2025
Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

June 25, 2025
KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

June 25, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

June 25, 2025
Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

June 25, 2025
Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

June 24, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

June 24, 2025
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

June 24, 2025
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

June 24, 2025
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.