• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

“Babu Gaskiya A Takardar Da Ke Alaƙanta Gwamnatin Zamfara Da ’Yan Bindiga”

by Musa Muhammad
8 months ago
in Labarai
0
“Babu Gaskiya A Takardar Da Ke Alaƙanta Gwamnatin Zamfara Da ’Yan Bindiga”
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata tarkardar ƙage, wacce aka ce ta fito ne daga gidan gwamnatin jihar Zamfara da ke Gusau, mai ɗauke da sa hannun Sakataren Gwamnatin Jihar, Alhaji Abubakar Nakwada, ta yi iƙirarin cewa Gwamna Dauda Lawal ya bayar da umurnin a saki Naira Biliyan 1,378,000,000 ga wasu manyan shugabannin ’yan bindiga.

Haka zalika, takardar ta yi zargin cewa kafafen yaɗa labarai irin su Sahara Reporters, Jackson Ude, da sauran su sun amfana da waɗannan kuɗaɗe.

  • Sojoji Sun Sheƙe Ƴan Ta’adda Masu  Yawa A Kaduna Da Zamfara
  • Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Tallafawa Majinyata 1000 Da Abinci Da Kuɗi

To amma yana da muhimmanci a fahimci cewa, dukkan waɗanda aka yi wa ƙazafi a cikin wannan takardar sharri, su ne waɗanda suka ɗauki labaran fallasa alaƙanta Bello Turji da Alhaji Bello Mattawalle, Ministan Tsaro, da badaƙalar Alhaji Bashir Hadejia da aka kama da laifin ɗaukar nauyin ta’addanci da safarar makamai da zinare da dai sauransu.

Wannan ne ta sa Sakataren gwamnatin Jihar Zamfara, Alhaji Abubakar Nakwada, yayin da yake mayar da martani kan wannan takarda, ya ce “Wannan takarda mara tushe ta alaƙanta gwamnatin Zamfara da kiran zaman lafiya da Bello Turji, wanda ya kasance sanannen shugaban ’yan bindiga ne ya yi.

Gwamnatin Gwamna Dauda Lawal ta yi kakkausar suka, inda ta musanta yin sulhu da ‘yan ta’adda, kuma ta jaddada cewa takardar, wani yunƙuri ne da aka ƙirƙira da gangan da nufin gurgunta ƙoƙarin da gwamnatin jihar ke yi na samar da tsaro.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

GORON JUMA’A 09/05/2025

Don haka a fahimci wannan labarin da cewa ƘARYA ce, kuma yaudara ce.

Ita ma jam’iyyar AAC ta Omoyele Sowore, wanda kuma shi ne mawallafin jaridar Sahararepoters, wacce kuma tana cikin waɗanda aka ce sun amfana da waɗannan kuɗaɗe, ta fito fili ta yi tofin Allah-tsine da ganin wannan takarda, wacce ta ce ƙarya ce tsagwaronta.

Ɗan takarar Shugaban ƙasa na Jam’iyyar ta AAC, wanda ya ke kuma shi ne shugabanta, Omoyele Sowore ya ce, “Ya wajaba a gare mu mu nusar da jama’a irin sabon salon farfagandar da Bola Tinubu ya fito da ita na zubar da mutuncin mani da mutunci, ni da SaharaReporters.

“Wata takardar cikin gida, wacce aka alaƙanta da Sakataren gwamnatin jihar Zamfara, tana nan tana yawo a tsakanin jama’a, aka ce wai an ware wasu maƙudan kuɗaɗe don a raba wa ‘yan ta’adda da wasu kafafen watsa labarai.

Sowore ya ce, wannan ƙarya ce, bai san da wani abu mai kama da haka ba.

Shi ma, ɗaya daga cikin waɗanda aka ambaci sunayen su a waccan ƙagaggar takarda, Jacson Ude, a shafin sa na tweeter (X), ya yi watsi da wannan batu, inda ya ɗora laifin kan tsohon Kwamishinan yaɗa labarai na gwamnatin Bello Matawalle.

Jackson Ude ya yi zargin cewa Tsohon Kwamishinan yaɗa labaran, ya kasance ya ɓoye kansa a wani wuri, inda ba abin da ya ke yi sai ƙage-ƙagen ƙarairayi kan duk waɗanda suka ya ƙi gwammatin Matawalle.

Don haka ya ce, wannan takarda sam ba ta da tushe balle makama, ƙarya ce tsagwaronta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BanditsTerroristZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

CIFIT: Dandalin Samun Wadata Ta Bai Daya

Next Post

Kungiyar Miyatti Allah Ta Haramta Kiwon Dare A Jihar Kwara

Related

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje
Labarai

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

25 minutes ago
GORON JUMA’A 09/05/2025
Labarai

GORON JUMA’A 09/05/2025

1 hour ago
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 
Labarai

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

2 hours ago
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci
Addini

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

3 hours ago
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote
Labarai

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

4 hours ago
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
Manyan Labarai

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

5 hours ago
Next Post
Kungiyar Miyatti Allah Ta Haramta Kiwon Dare A Jihar Kwara

Kungiyar Miyatti Allah Ta Haramta Kiwon Dare A Jihar Kwara

LABARAI MASU NASABA

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.