• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Sulhu Tsakaninmu Da ‘Yan Fashin Daji -Gwamnatin Zamfara

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Babu Sulhu Tsakaninmu Da ‘Yan Fashin Daji -Gwamnatin Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu daga cikin ‘yan majalisar jihar Zamfara sun ce babu wani dalili da zai sa gwamnatin jihar ta yi sulhu da ‘yan fashi a jihar.

Honarabul Hamisu A Faru, mai wakiltar mazabar Bukkuyum ta Kudu a majalisar dokokin jihar ne, ya bayyana hakan cikin hirarsa da BBC Hausa.

  • Ganduje Na Iya Maye Gurbin Adamu A Matsayin Shugaban Jam’iyyar APC Na Kasa
  • A Karon Farko Bayan Barin Mulki, Buhari Ya Halarci Taro A Katsina

Ya ce “Babu yadda za a yi sulhu da mutumin da bai san Allah ba”.

Wannan na zuwa ne kwanaki kadan da ‘yan fashin daji suka kori mazauna wani kauye gaba dayansu a cikin daya daga kananan hukumomin da yake wakilta kana suka mayar da shi sansaninsu.

Dan Majalisar ya ce “Gwamnan jihar ya fito ya kalubalanci duk wani mai neman a yi sulhu da ‘yan fashin” wanda hakan ne ya kara musu karfin gwiwa a wannan tafiya.

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A YaÆ™i Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

Ya ce akwai firgici a halin da ake ciki a jihar yanzu, domin barayin sun tsallaka titin Gurusu sun bi Barayar zaki sun tsallaka Gulbi sun je wani kauyen Rafin Gero da ake ce masa Gyado sun yi sansani, yau tsawon kwana 10 kenan.

Ya kara da cewa kalubalen da ake fuskanta a yanzu shi ne an shiga damuna, lokacin da yaki da wadannan bata-gari ke da wuya.

“Da yawan dazuka itatuwansu sun yi kore sun zama duhuwa, tsakaninka da mutane ba tazara mai yawa amma duhu ba zai barku kuga juna ba.

“Shekaran jiya sun shiga kauyukan Ruwan rana da Yashi sun kone shaguna da kuma dukiya mai yawa,” in ji Hamisu A Faru.

‘Yan fashin daji sun dauki tsawon shekaru suna kai hare-hare a jihar Zamfara da ma jihohin da suka yi makwabtaka da ita irin su; Katsina, Sakkwato da Kaduna.

Lamarin da ya yi sanadin mutuwar dubban mutane tare da sanya da dama zama ‘yan gudun hijira.

Sai dai wasu na ganin yin sulhu da ‘yan fashin dajin na iya kawo sauki ga hare-haren nasu, lamarin da ya sanya gwamnatin jihar kin amsar wannan shawara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan Fashin dajiKadunaKatsinaSakkwatoSulhuZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsarin Zuba Jari A Nijeriya Da Cikar NIS Shekara 60 Da Kafuwa

Next Post

An Rufe Makarantu A Kenya Saboda Zanga-Zangar Tsadar Rayuwa

Related

Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina
Manyan Labarai

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A YaÆ™i Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

3 hours ago
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje
Da É—umi-É—uminsa

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

15 hours ago
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Rasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi
Da É—umi-É—uminsa

SDP: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Wa El-Rufai Shaguɓe Da Ayyana Shi A Matsayin Ɗan Gudun Hijirar Siyasa

17 hours ago
Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja
Manyan Labarai

Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja

19 hours ago
Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno
Manyan Labarai

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno

21 hours ago
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
Manyan Labarai

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

2 days ago
Next Post
An Rufe Makarantu A Kenya Saboda Zanga-Zangar Tsadar Rayuwa

An Rufe Makarantu A Kenya Saboda Zanga-Zangar Tsadar Rayuwa

LABARAI MASU NASABA

EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan HaÆ™ar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Akwa Ibom

EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan HaÆ™ar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Akwa Ibom

July 29, 2025
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A YaÆ™i Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

July 29, 2025
An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

July 28, 2025
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

July 28, 2025
Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

July 28, 2025
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

July 28, 2025
An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

July 28, 2025
Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

July 28, 2025
Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

July 28, 2025
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

July 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.