ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Sulhu Tsakaninmu Da ‘Yan Fashin Daji -Gwamnatin Zamfara

by Sadiq
2 years ago
Zamfara

Wasu daga cikin ‘yan majalisar jihar Zamfara sun ce babu wani dalili da zai sa gwamnatin jihar ta yi sulhu da ‘yan fashi a jihar.

Honarabul Hamisu A Faru, mai wakiltar mazabar Bukkuyum ta Kudu a majalisar dokokin jihar ne, ya bayyana hakan cikin hirarsa da BBC Hausa.

  • Ganduje Na Iya Maye Gurbin Adamu A Matsayin Shugaban Jam’iyyar APC Na Kasa
  • A Karon Farko Bayan Barin Mulki, Buhari Ya Halarci Taro A Katsina

Ya ce “Babu yadda za a yi sulhu da mutumin da bai san Allah ba”.

ADVERTISEMENT

Wannan na zuwa ne kwanaki kadan da ‘yan fashin daji suka kori mazauna wani kauye gaba dayansu a cikin daya daga kananan hukumomin da yake wakilta kana suka mayar da shi sansaninsu.

Dan Majalisar ya ce “Gwamnan jihar ya fito ya kalubalanci duk wani mai neman a yi sulhu da ‘yan fashin” wanda hakan ne ya kara musu karfin gwiwa a wannan tafiya.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

Ya ce akwai firgici a halin da ake ciki a jihar yanzu, domin barayin sun tsallaka titin Gurusu sun bi Barayar zaki sun tsallaka Gulbi sun je wani kauyen Rafin Gero da ake ce masa Gyado sun yi sansani, yau tsawon kwana 10 kenan.

Ya kara da cewa kalubalen da ake fuskanta a yanzu shi ne an shiga damuna, lokacin da yaki da wadannan bata-gari ke da wuya.

“Da yawan dazuka itatuwansu sun yi kore sun zama duhuwa, tsakaninka da mutane ba tazara mai yawa amma duhu ba zai barku kuga juna ba.

“Shekaran jiya sun shiga kauyukan Ruwan rana da Yashi sun kone shaguna da kuma dukiya mai yawa,” in ji Hamisu A Faru.

‘Yan fashin daji sun dauki tsawon shekaru suna kai hare-hare a jihar Zamfara da ma jihohin da suka yi makwabtaka da ita irin su; Katsina, Sakkwato da Kaduna.

Lamarin da ya yi sanadin mutuwar dubban mutane tare da sanya da dama zama ‘yan gudun hijira.

Sai dai wasu na ganin yin sulhu da ‘yan fashin dajin na iya kawo sauki ga hare-haren nasu, lamarin da ya sanya gwamnatin jihar kin amsar wannan shawara.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

November 14, 2025
Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

November 14, 2025
Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya
Manyan Labarai

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

November 14, 2025
Next Post
An Rufe Makarantu A Kenya Saboda Zanga-Zangar Tsadar Rayuwa

An Rufe Makarantu A Kenya Saboda Zanga-Zangar Tsadar Rayuwa

LABARAI MASU NASABA

Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

November 14, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

November 14, 2025
Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

November 14, 2025
Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

November 14, 2025
Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

November 14, 2025
Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

November 14, 2025
Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.