• English
  • Business News
Thursday, June 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Wata Kafa Na Yin Magudin Zabe A 2023 – INEC

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Babu Wata Kafa Na Yin Magudin Zabe A 2023 – INEC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta kara jaddada cewa babu wata kafa na yin magudin zabe a 2023.

A cewar hukumar, magudin zabe zai yi matukar wahala sakamakon yadda hukumar da shirya tsaf wajen gudanar da sahihin zabe a 2023.

  • Ba A Aiwatar Da Wasu Matakai Na Yaki Da COVID-19 Domin Muzgunawa Al’ummar Uygur Ba
  • Nijeriya Za Ta Fara Fitar Da Shinkafa Zuwa Masar

Sabuwar kwamishinar zaben Jihar Ebonyi, Misis Onyeka Ugochi ita ta bayyana hakan a Abakaliki lokacin da take zantawa da ‘yan jarida da kungiyoyin fararen hula.

“Magudin zabe ba zai taba kasancewa ba daga bangaren INEC. Sai dai magudin zabe ya kasance ta bangaren ‘yan siyasa. Mun yi iya bakin kokarinmu wajen tsare muhimman abubuwa kamar fitar da takardar sakamakon zabe da sauran abubuwa.

“A yanzu haka tsarin yana da matukar yi musu wahala wajen yin magudi sakamakon yin amfani da na’urar tantance masu jefa kuri’a. Ba za a iya tsallake na’urrarmu ba ko kuma har a iya kashe dukkan naurar da muke amfani da su lokacin gudanar da zabe.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

“Yana da matukar wahala a iya yin magudin zabe a yanzu. Wannan lokaci ne da ‘yan jarida da kungiyoyin fararen huda za su yi aiki kafada da kafada wajen tsaftace al’umma. A bayyane muke gudanar da ayyukanmu, za mu yi iya bakin kokarinmu wajen ganin komi ya tafi yadda aka tsara.

“Za mu mayar da dukkan abubuwan da muka rasa a lokacin farmaki. Yana da matukar muhummanci ‘yan jarida su mara mana baya wajen gudanar da ayyukanmu yadda ya kamata,” in ji ta.

Kwamishinar da ce a daidai lokacin da ‘yan jarida suke da rawar da za su taka na sanar da ‘yan kasa kan gasa a tsakanin jam’iyyun siyasa da ‘yan takara da kuma manufofinsu, haka kuma suke da shi wajen fadakar da mutane domin amsar katin zabe kafin lokacin gudanar da zaben 2023.

Ta kuma jaddada wa ‘yan jarida da kungiyoyin fararen hula da sauran kawaye da kuma daukacin mutanen Jihar Ebonyi cewa a karkashin kulawarta hukumar za ta gudanar da sahihin zabe da zai kubuta daga rikice-rikicen zabe a jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: INECZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba A Aiwatar Da Wasu Matakai Na Yaki Da COVID-19 Domin Muzgunawa Al’ummar Uygur Ba

Next Post

Sana’ar Safarar Dabbobi A Halin Yanzu Sai Godiya -Aminu Isimaila

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

2 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

2 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

3 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

4 weeks ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
Sana’ar Safarar Dabbobi A Halin Yanzu Sai Godiya -Aminu Isimaila

Sana’ar Safarar Dabbobi A Halin Yanzu Sai Godiya -Aminu Isimaila

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

June 26, 2025
Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

June 25, 2025
Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

June 25, 2025
Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

June 25, 2025
MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

June 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

June 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

June 25, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa

Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa

June 25, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Katse Hanyar Maiduguri Zuwa Damboa

Mutane 4 Sun Mutu, 10 Sun Jikkata Yayin Da Wata Mota Ta Taka Bam A Borno

June 25, 2025
Shawarar Gudanar Da Harkokin AI Na Duniya Na Jagorantar Ci Gaban Wayewar Kan Dan Adam Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani

Shawarar Gudanar Da Harkokin AI Na Duniya Na Jagorantar Ci Gaban Wayewar Kan Dan Adam Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani

June 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.