• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Wata Kafa Na Yin Magudin Zabe A 2023 – INEC

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
INEC

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta kara jaddada cewa babu wata kafa na yin magudin zabe a 2023.

A cewar hukumar, magudin zabe zai yi matukar wahala sakamakon yadda hukumar da shirya tsaf wajen gudanar da sahihin zabe a 2023.

  • Ba A Aiwatar Da Wasu Matakai Na Yaki Da COVID-19 Domin Muzgunawa Al’ummar Uygur Ba
  • Nijeriya Za Ta Fara Fitar Da Shinkafa Zuwa Masar

Sabuwar kwamishinar zaben Jihar Ebonyi, Misis Onyeka Ugochi ita ta bayyana hakan a Abakaliki lokacin da take zantawa da ‘yan jarida da kungiyoyin fararen hula.

“Magudin zabe ba zai taba kasancewa ba daga bangaren INEC. Sai dai magudin zabe ya kasance ta bangaren ‘yan siyasa. Mun yi iya bakin kokarinmu wajen tsare muhimman abubuwa kamar fitar da takardar sakamakon zabe da sauran abubuwa.

“A yanzu haka tsarin yana da matukar yi musu wahala wajen yin magudi sakamakon yin amfani da na’urar tantance masu jefa kuri’a. Ba za a iya tsallake na’urrarmu ba ko kuma har a iya kashe dukkan naurar da muke amfani da su lokacin gudanar da zabe.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

“Yana da matukar wahala a iya yin magudin zabe a yanzu. Wannan lokaci ne da ‘yan jarida da kungiyoyin fararen huda za su yi aiki kafada da kafada wajen tsaftace al’umma. A bayyane muke gudanar da ayyukanmu, za mu yi iya bakin kokarinmu wajen ganin komi ya tafi yadda aka tsara.

“Za mu mayar da dukkan abubuwan da muka rasa a lokacin farmaki. Yana da matukar muhummanci ‘yan jarida su mara mana baya wajen gudanar da ayyukanmu yadda ya kamata,” in ji ta.

Kwamishinar da ce a daidai lokacin da ‘yan jarida suke da rawar da za su taka na sanar da ‘yan kasa kan gasa a tsakanin jam’iyyun siyasa da ‘yan takara da kuma manufofinsu, haka kuma suke da shi wajen fadakar da mutane domin amsar katin zabe kafin lokacin gudanar da zaben 2023.

Ta kuma jaddada wa ‘yan jarida da kungiyoyin fararen hula da sauran kawaye da kuma daukacin mutanen Jihar Ebonyi cewa a karkashin kulawarta hukumar za ta gudanar da sahihin zabe da zai kubuta daga rikice-rikicen zabe a jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
Sana’ar Safarar Dabbobi A Halin Yanzu Sai Godiya -Aminu Isimaila

Sana’ar Safarar Dabbobi A Halin Yanzu Sai Godiya -Aminu Isimaila

LABARAI MASU NASABA

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.