ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu wata Yarjejeniya Da Aka Gindaya Cewa Za A Ba Tinubu Shugaban Kasa Bayan Buhari -Yerima

by Muhammad
3 years ago
Babu

Tsohon gwamnan jihar Zamfara, Sanata Ahmad Sani Yerima, ya ce babu wata yarjejeniya tsakanin jam’iyyar APC da Ahmad Tinubu, na ba shi takarar shugaban kasar nan bayan mulkin shugaba Muhammadu Buhari.

Yerima, wanda kuma dan takarar shugaban kasa ne a jam’iyyar APC mai mulki, ya bayyana hakan a cikin shirin siyasa na Trust Tv, Daily Politics, a daren Juma’a.

  • Kwamitin tantance ‘Yan Takarar Shugaban Kasa Na APC Ya Yi Watsi Da ‘Yan Takara 10 Cikin 23
  • 2023: Buhari Zai Gana Da Masu Ruwa Da Tsaki Don Fitar Da Magajinsa Gabanin Taron APC

Tinubu, yayin da yake zantawa da wakilan jam’iyyar a jihar Ogun a ranar Alhamis, ya ce lokaci ya yi da zai zama shugaban Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Tsohon gwamnan jihar Legas ya kuma bayyana yadda ya goyi bayan Buhari a takararsa ta shugaban kasa tare da ba da ba Osinbajo mukamin mataimakin shugaban kasa, wanda shi ma a halin yanzu ke zawarcin mukamin shugaban kasa bayan ya gama mataimakin shugaban kasa karo na biyu.

Idan zamu iya tunawa, Jam’iyyar Tinubu, (ACN) ta narke wuri guda da sauran Jam’iyyu a watan Fabrairun 2013, tare da (CPC) da (ANPP) – da kuma wani bangare na (APGA) domin kafa jam’iyyar APC tare da Buhari daga jam’iyyar CPC aka ba shi damar tsayawa takarar babban mukami.

LABARAI MASU NASABA

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

An yi imanin cewa akwai yarjejeniyar da ACN ta yi na cewa za ta fitar da dan takarar shugaban kasa na gaba bayan mulkin Buhari.

Sai dai Yerima ya ce babu wani rahoto da ke nuna an kulla irin wannan yarjejeniya da jam’iyyar.

“Babu wata yarjejeniya da t tabbatar da haka, a lokacin wanene shugaban jam’iyyar? Da farko muna da Cif Bisi Akande, daga baya kuma, muna da John Oyegun, kuma a yau muna da Sanata Abdullahi Adamu, muna da [Mai Mala] Buni a cikin tafiyar da dai sauransu.

“To, ko Cif Bisi Akande ne ya zauna da wasu mutane? Duk wani hukunci da aka dauka a wajen tsarin jam’iyyar ba a amince da shi ba. Jam’iyyar tana da kwamitin ayyuka na kasa, jam’iyyar kuma tana da abin da muke kira NEC kuma akwai bangaren yanke shawara gaba daya wato babban taron kasa.

Ya ci gaba da cewa, “Duk hukuncin da ba a dauka a cikin tsarin jam’iyyar ba, ba hukunci ba ne. Ba za ku iya samun fahimta da mutum ba kuma ku ce ‘hakan zai faru. Idan jam’iyya tana son yanke shawara, ko dai kwamitin ayyuka na kasa ne, ko hukumar zabe ta yanke.

“Idan Yarjejeniyar ta yanke shawara, ba za a iya canza ta ba. Amma za a iya sake duba yanke shawara bisa kowane yanayi. Ko da akwai wannan fahimtar, yanayin yau na iya bambanta da yadda yake lokacin da aka cimma wannan fahimtar. ”

Jam’iyyar APC ta tsayar da ranar 6 ga watan Yuni a matsayin ranar babban taronta a birnin tarayya Abuja, inda za ta zabi dan takararta na shugaban kasa a zaben 2023.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC
Manyan Labarai

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa
Siyasa

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

November 15, 2025
Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP
Siyasa

Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

November 12, 2025
Next Post
Mene Ne Bambancin Wadannan Ruwan Guda Biyu Masu Fitowa Daga Gaban Mace?

Mene Ne Bambancin Wadannan Ruwan Guda Biyu Masu Fitowa Daga Gaban Mace?

LABARAI MASU NASABA

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.