• English
  • Business News
Monday, October 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Badakalar Kudi: PDP Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Binciki Buratai

by Sadiq
3 years ago
Buratai

Jam’iyyar PDP ta yi kira ga shugaban kasa Muhammadu Buhari da ya sa a binciki tsohon babban hafsan sojin kasa (COAS) kuma Ambasada a Jamhuriyar Benin, Laftanar-Janar Tukur Buratai (mai ritaya) kan almundahanar Naira Biliyan 1.8 na sayen makamai.

A cikin wata sanarwa da kakakinta, Debo Ologunagba, ya fitar, jam’iyyar ta ce ya kamata a binciki Buratai kan zargin badakalar Naira Biliyan 1.8 da hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta ICPC ta kwato a wasu kadarorin Abuja.

  • Na Bai Wa Peter Obi Damar Zama Abokin Takarata – Kwankwaso
  • Rashin Yaba Kwalliyar Mace Daga Mijinta: A Ina Gizo Yake Sakar?

PDP ta ce bukatar binciken Buratai ya ta’allaka ne kan ikirarin da mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Janar Babagana Monguno ya yi baya ficewar Janar Buratai a matsayin COAS na cewa dala biliyan 1 da aka karbo daga asusun kasa a karkashin jam’iyyar APC. Ba a iya gano yadda ake gudanar da sayan makaman yaki da ta’addanci ba.

Jam’iyyar ta ce wannan ikirari da hukumar ta NSA ta yi ya kara nuna shakku kan zargin wawure kudaden da ake son yi wa jami’an tsaronmu kayan aiki, inda ta kara da cewa “irin wannan cin hanci da rashawa a karkashin gwamnatin APC ya haifar da karuwar hare-haren ta’addanci ba tare da tangarda ba, da kashe-kashen jama’a da kuma asarar rayuka. da yawa daga cikin mayakanmu na gaba a cikin shekaru bakwai da suka gabata.”

Jam’iyyar adawar ta kuma ce rahotannin sace-sacen da shugabannin jam’iyyar APC da mukarrabansu ke yi a ma’aikatu da hukumomin gwamnati na kara tabbatar da cewa gwamnatin APC ta zama mafakar masu wawure dukiyar kasa.

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

“Bugu da kari, kwanan nan da aka fallasa wawure Naira biliyan 80 da Akanta-Janar na Tarayya, Ahmed Idris ya yi, wanda bincike ya yi sanyi a halin yanzu ana zargin jami’an gwamnatin APC ne suka kitsa wani abu a kai.

“Jam’iyyar PDP da ke tsaye ga ‘yan Nijeriya, ta bukaci Janar Buratai ya dawo kasar nan  don ya fuskanci bincike domin ya wanke sunansa.

“Wannan shi ne saboda duk wani zargin da ya shafi wawure kudaden da ake nufi da yaki da ta’addanci yana da matukar muhimmanci ga kasar nan. Dole ne a yu bincike sosai kuma duk wanda aka samu yana da hannu ya fuskanci cikakken hukuncin doka, “in ji jam’iyyar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

October 27, 2025
Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum
Manyan Labarai

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

October 26, 2025
Next Post
2023: PDP Na Bukatar Hadi Kai Don Kayar Da APC – Makarfi

2023: PDP Na Bukatar Hadi Kai Don Kayar Da APC – Makarfi

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

October 27, 2025
Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

October 27, 2025
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Ba Za A Samu Ƙarancin Man Fetur A Lokutan Bukukuwan Ƙarshen Shekara Ba – Dangote 

October 27, 2025
An Zaɓi Birgediya Janar Yake A Matsayin Sarkin Sayawa Na Farko Duk Da Zanga-zanga 

An Zaɓi Birgediya Janar Yake A Matsayin Sarkin Sayawa Na Farko Duk Da Zanga-zanga 

October 27, 2025
Buratai

Tsohon Gwamnan Jigawa, Lamido Ya Bayyana Aniyar Takarar Shugabancin Jam’iyyar PDP Na Ƙasa

October 27, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

October 27, 2025
Hatsarin Jiragen Ruwa

Matasa 5 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Gombe

October 27, 2025
Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

October 26, 2025
Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

October 26, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.