• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Badakalar Kudi: PDP Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Binciki Buratai

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Badakalar Kudi: PDP Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Binciki Buratai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar PDP ta yi kira ga shugaban kasa Muhammadu Buhari da ya sa a binciki tsohon babban hafsan sojin kasa (COAS) kuma Ambasada a Jamhuriyar Benin, Laftanar-Janar Tukur Buratai (mai ritaya) kan almundahanar Naira Biliyan 1.8 na sayen makamai.

A cikin wata sanarwa da kakakinta, Debo Ologunagba, ya fitar, jam’iyyar ta ce ya kamata a binciki Buratai kan zargin badakalar Naira Biliyan 1.8 da hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta ICPC ta kwato a wasu kadarorin Abuja.

  • Na Bai Wa Peter Obi Damar Zama Abokin Takarata – Kwankwaso
  • Rashin Yaba Kwalliyar Mace Daga Mijinta: A Ina Gizo Yake Sakar?

PDP ta ce bukatar binciken Buratai ya ta’allaka ne kan ikirarin da mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Janar Babagana Monguno ya yi baya ficewar Janar Buratai a matsayin COAS na cewa dala biliyan 1 da aka karbo daga asusun kasa a karkashin jam’iyyar APC. Ba a iya gano yadda ake gudanar da sayan makaman yaki da ta’addanci ba.

Jam’iyyar ta ce wannan ikirari da hukumar ta NSA ta yi ya kara nuna shakku kan zargin wawure kudaden da ake son yi wa jami’an tsaronmu kayan aiki, inda ta kara da cewa “irin wannan cin hanci da rashawa a karkashin gwamnatin APC ya haifar da karuwar hare-haren ta’addanci ba tare da tangarda ba, da kashe-kashen jama’a da kuma asarar rayuka. da yawa daga cikin mayakanmu na gaba a cikin shekaru bakwai da suka gabata.”

Jam’iyyar adawar ta kuma ce rahotannin sace-sacen da shugabannin jam’iyyar APC da mukarrabansu ke yi a ma’aikatu da hukumomin gwamnati na kara tabbatar da cewa gwamnatin APC ta zama mafakar masu wawure dukiyar kasa.

Labarai Masu Nasaba

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

“Bugu da kari, kwanan nan da aka fallasa wawure Naira biliyan 80 da Akanta-Janar na Tarayya, Ahmed Idris ya yi, wanda bincike ya yi sanyi a halin yanzu ana zargin jami’an gwamnatin APC ne suka kitsa wani abu a kai.

“Jam’iyyar PDP da ke tsaye ga ‘yan Nijeriya, ta bukaci Janar Buratai ya dawo kasar nan  don ya fuskanci bincike domin ya wanke sunansa.

“Wannan shi ne saboda duk wani zargin da ya shafi wawure kudaden da ake nufi da yaki da ta’addanci yana da matukar muhimmanci ga kasar nan. Dole ne a yu bincike sosai kuma duk wanda aka samu yana da hannu ya fuskanci cikakken hukuncin doka, “in ji jam’iyyar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Badakalar Kudin MakamaiBincikeBurataiGwamnatin TarayyaPDPTsohon Hafsan Sojin Kasan NijeriyaTuhuma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jam’iyyar Labour Party Ba Za Ta Lashe Zaben 2023 Ba – Kwankwaso

Next Post

2023: PDP Na Bukatar Hadi Kai Don Kayar Da APC – Makarfi

Related

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

4 hours ago
Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 
Manyan Labarai

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

13 hours ago
Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare
Manyan Labarai

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

1 day ago
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
Da ɗumi-ɗuminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

2 days ago
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO
Manyan Labarai

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

2 days ago
Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu
Manyan Labarai

Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu

2 days ago
Next Post
2023: PDP Na Bukatar Hadi Kai Don Kayar Da APC – Makarfi

2023: PDP Na Bukatar Hadi Kai Don Kayar Da APC – Makarfi

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

August 4, 2025
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

August 4, 2025
Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

August 4, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

August 4, 2025
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

August 4, 2025
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

August 4, 2025
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

August 4, 2025
Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.