• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Badaru Na Da Kwarewar Jagorantar Ma’aikatar Tsaro – ANA

by Maryam Rabiu, Abuja
2 years ago
Badaru

Wata kungiyar siyasa da zamantakewa mai suna Arewa New Agenda (ANA), ta bayyana goyon bayanta ga sabon ministan tsaro da aka nada, Mohammed Badaru Abubakar, inda ta ce masu sukar nadin nasa ba su da masaniya kan kwarewar da yake da ita.

Shugaban kungiyar Sanata Ahmad Abubakar MoAllahyidi ne, ya bayyana haka a wani taron manema labarai a Abuja ranar Alhamis.

  • Ana Zargin Gwamnatin Jihar Katsina Da Yin Rufa-Rufa Da Kudaden Ƙananan Hukumomi
  • Rushewar Gini: Wike Ya Umarci A Cafko Mamallakin Ginin Cikin Gaggawa

LEADERDHIP ta ruwaito cewa, ANA ta yi hasashen yadda yankin Arewa zai ci gaba da habaka.

Yayin da sabbin ministocin suka shiga zama a ofisoshinsu, ANA ta nuna rashin jin dadinta kan abin da ta kira sukar rashin adalci da ake yi wa wasu Ministocin, wadanda wasu suka fake da rigar Addini da kabilanci wajen sukarsu.

MoAllahyidi ya ce: “Mohammed Abubakar Badaru, sabon ministan tsaro da aka nada, an ware shi ana sukarsa ba komai ba ne face rashin adalci.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

“Shekaru takwas da Badaru ya yi a matsayin Gwamnan Jihar Jigawa abin koyi ne na tabbatar da tsaro, zaman lafiya, da zaman tare duk da raunin da jihar ke fama da shi.

“Duk da kasancewar jihar Jigawa makwabciyar kasashe da jihohi masu fama da rashin tsaro, jihar na daya daga cikin jahohin Arewa da ba su taba fuskantar matsalar rashin tsaro ba.

“Kungiyar ta ga ya dace ya jagoranci ma’aikatar tsaro, idan aka yi la’akari da tarihinsa na kare martabar yankinsa.

“Nasarar da Badaru ya samu a fagen jama’a da kuma na sirri ya nuna kwarewarsa kan wannan fage.”

ANA ta jaddada wajibcin samun goyon baya da mutunta shugabanci, inda ta yi watsi da duk wani kira na sauya Badaru daga mukamin ministan tsaro

MoAllahyidi ya kara da cewa: “ANA ta kuduri aniyar samar da zaman lafiya yayin da Najeriya ke ci gaba da kokarin inganta kasa.

“Babu shakka, Nijeriya tana cikin wani yanayi. Bukatar ministocin masu tunani da za su iya amfani da albarkatun dan Adam da na kayan aiki don inganta rayuwar ‘yan kasa.”

ANA ta taya ministoci 45 da aka rantsar a baya-bayan nan murna, sannan ta bukace su da su yi kokari wajen samar da bambamci, yana mai cewa nadin nasu ya ba da wata sabuwar dama ta ciyar al’umma gaba.

Sai dai ANA ta yi kira ga ministocin yankin Arewa da su yi aiki tukuru domin ci gaban Arewa da ma Nijeriya baki daya.

Kungiyar ta jaddada bukatar fifita hangen nesa fiye da bukatun kashin kai, inda ta bayyana manyan manufofin da shugaban kasa ya gindaya.

ANA ta jaddada muhimmancin ministocin da su yi hulda da jama’a don fahimtar bukatunsu tare da shigar da su cikin ajandar gwamnatin Shugaba Tinubu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Asuu
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro
Labarai

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
majalisar kasa
Labarai

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
Next Post
BRICS Na Taka Rawar Gani Ga Ci Gaban Nahiyar Afirka

BRICS Na Taka Rawar Gani Ga Ci Gaban Nahiyar Afirka

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Asuu

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

October 29, 2025
Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

October 29, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

October 29, 2025
COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.