ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

BRICS Na Taka Rawar Gani Ga Ci Gaban Nahiyar Afirka

by CMG Hausa
3 years ago
brics

Ga duk mai bibiyar yanayin ci gaban da ake samu karkashin hadakar kungiyar bunkasa tattalin arzikin kasashen BRICS, zai tabbatar da cewa kungiyar ta haifar da kyakkyawan fatan cimma moriyar juna, matakin da ke kara kyautata moriyar kasashen Afirka, da sauran kasashe masu tasowa. 

Kungiyar BRICS mai kunshe da kasashen Brazil, da Rasha, da Indiya, da Sin da Afirka ta kudu, wadda a yanzu ke shirin karkare taron shugabanninta karo na 15 a Afirka ta kudu, ta tabbatar da matsayinta na adawa da ra’ayin cacar baka, da danniya, ta kuma mai da hankali ga yayata akidun gudanar da cudanya tsakanin dukkanin sassa, da martaba juna, da hadin gwiwa, da rike gaskiya da adalci, ta hanyar samar da wani ginshiki na daban, wanda duniyar yau za ta iya dogaro da shi.

  • Me Ya Sa Nijeriya Ke Neman Shiga Tsarin BRICS?

Ya zuwa yanzu, kasashe mambobin kungiyar BRICS ne ke da sama da kaso 40 bisa dari na jimillar adadin al’ummar duniya, da kaso 20 bisa dari na darajar cinikayyar duniya, yayin da kasashe mambobin take janyo kaso 25 bisa dari na daukacin jarin waje da ake zubawa a duniya.

ADVERTISEMENT

La’akari da alakar kut da kut ta cinikayya, da musaya tsakanin dukkanin wadannan kasashe mambobin BRICS da kasashen nahiyar Afirka, da kuma tasirin alkaluman tattalin arzikinsu ga bunkasar tattalin arzikin duniya baki daya, za mu iya gane dalilan da suka sanya ci gaban BRICS ke taka rawar gani ga ci gaban Afirka, ta hanyoyi masu yawa.

BRICS ta riga ta gabatarwa duniya wata dama ta cimma alherai, musamman ga kasashen da tattalin arzikinsu ke saurin bunkasa, da kasashe masu tasowa, ta kuma ingiza hadin gwiwarsu, tare da zama wani muhimmin dandali na kyautata ci gaban kasashe masu tasowa ta fuskar dinke dukkanin sassa, yayin tafiya kan tafarkin bunkasuwa tare.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Wadannan dalilai ne suka sanya a halin yanzu, karin kasashen Afirka da suka hada da Najeriya, da Aljeriya da Masar, suka shiga cikin jimillar kasashe 23 dake fatan zama sabbin mambobin wannan kungiya mai daraja.

Yayin da wasu kasashen duniya ke aiwatar da matakan haifar da baraka ga duniya, da kafa tsarin rarrabuwar kawuna, da fadada jibge sojoji, da kafa kawance a fannin, da nufin tabbatar da ikon kashin kai, a hannu guda kungiyar BRICS, na kara mayar da hankali ga bunkasa zaman lafiyar duniya, da yayata manufofin ci gaban bai daya na kasashen duniya, ciki har da kasashen Afirka.

Don haka dai muna iya cewa, yayin da kasashen Afirka ke fafutukar raya kansu, da kaucewa duk wani yanayi na koma baya, kungiyar BRICS ta zama wata hanya mai inganci da kasashe na Afirka za su ci gaba da bi, domin kaiwa ga tudun mun tsira. (Saminu Hassan)

brics
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
‘Yan Boko Haram Sun Saki Mata 48 Da Suka Yi Garkuwa Da Su A Borno

'Yan Boko Haram Sun Saki Mata 48 Da Suka Yi Garkuwa Da Su A Borno

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.