ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

BRICS Na Taka Rawar Gani Ga Ci Gaban Nahiyar Afirka

by CMG Hausa
3 years ago
brics

Ga duk mai bibiyar yanayin ci gaban da ake samu karkashin hadakar kungiyar bunkasa tattalin arzikin kasashen BRICS, zai tabbatar da cewa kungiyar ta haifar da kyakkyawan fatan cimma moriyar juna, matakin da ke kara kyautata moriyar kasashen Afirka, da sauran kasashe masu tasowa. 

Kungiyar BRICS mai kunshe da kasashen Brazil, da Rasha, da Indiya, da Sin da Afirka ta kudu, wadda a yanzu ke shirin karkare taron shugabanninta karo na 15 a Afirka ta kudu, ta tabbatar da matsayinta na adawa da ra’ayin cacar baka, da danniya, ta kuma mai da hankali ga yayata akidun gudanar da cudanya tsakanin dukkanin sassa, da martaba juna, da hadin gwiwa, da rike gaskiya da adalci, ta hanyar samar da wani ginshiki na daban, wanda duniyar yau za ta iya dogaro da shi.

  • Me Ya Sa Nijeriya Ke Neman Shiga Tsarin BRICS?

Ya zuwa yanzu, kasashe mambobin kungiyar BRICS ne ke da sama da kaso 40 bisa dari na jimillar adadin al’ummar duniya, da kaso 20 bisa dari na darajar cinikayyar duniya, yayin da kasashe mambobin take janyo kaso 25 bisa dari na daukacin jarin waje da ake zubawa a duniya.

ADVERTISEMENT

La’akari da alakar kut da kut ta cinikayya, da musaya tsakanin dukkanin wadannan kasashe mambobin BRICS da kasashen nahiyar Afirka, da kuma tasirin alkaluman tattalin arzikinsu ga bunkasar tattalin arzikin duniya baki daya, za mu iya gane dalilan da suka sanya ci gaban BRICS ke taka rawar gani ga ci gaban Afirka, ta hanyoyi masu yawa.

BRICS ta riga ta gabatarwa duniya wata dama ta cimma alherai, musamman ga kasashen da tattalin arzikinsu ke saurin bunkasa, da kasashe masu tasowa, ta kuma ingiza hadin gwiwarsu, tare da zama wani muhimmin dandali na kyautata ci gaban kasashe masu tasowa ta fuskar dinke dukkanin sassa, yayin tafiya kan tafarkin bunkasuwa tare.

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Wadannan dalilai ne suka sanya a halin yanzu, karin kasashen Afirka da suka hada da Najeriya, da Aljeriya da Masar, suka shiga cikin jimillar kasashe 23 dake fatan zama sabbin mambobin wannan kungiya mai daraja.

Yayin da wasu kasashen duniya ke aiwatar da matakan haifar da baraka ga duniya, da kafa tsarin rarrabuwar kawuna, da fadada jibge sojoji, da kafa kawance a fannin, da nufin tabbatar da ikon kashin kai, a hannu guda kungiyar BRICS, na kara mayar da hankali ga bunkasa zaman lafiyar duniya, da yayata manufofin ci gaban bai daya na kasashen duniya, ciki har da kasashen Afirka.

Don haka dai muna iya cewa, yayin da kasashen Afirka ke fafutukar raya kansu, da kaucewa duk wani yanayi na koma baya, kungiyar BRICS ta zama wata hanya mai inganci da kasashe na Afirka za su ci gaba da bi, domin kaiwa ga tudun mun tsira. (Saminu Hassan)

brics
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji
Daga Birnin Sin

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina
Daga Birnin Sin

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Next Post
‘Yan Boko Haram Sun Saki Mata 48 Da Suka Yi Garkuwa Da Su A Borno

'Yan Boko Haram Sun Saki Mata 48 Da Suka Yi Garkuwa Da Su A Borno

LABARAI MASU NASABA

Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC

Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC

June 26, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

June 26, 2026
Noma

Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba

June 26, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

June 26, 2026
Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

June 26, 2026
Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.