• English
  • Business News
Thursday, June 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rushewar Gini: Wike Ya Umarci A Cafko Mamallakin Ginin Cikin Gaggawa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Rushewar Gini: Wike Ya Umarci A Cafko Mamallakin Ginin Cikin Gaggawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Biyo bayan rushewar wani gini mai hawa biyu a kan babban hanyar layin Legas da ke gundumar Garki II a Abuja wajajen karfe 11:45 na daren ranar Laraba, ministan birnin tarayya, Nyesom Wike, ya bada umarnin a gaggauta kamo wanda ya mallaki ginin da ya rushe din. 

Wike, wanda ya bada umarnin a lokacin da ya ziyarci wurin da lamarin ya faru da safiyar ranar Alhamis, ya jinjina da aikin ceto da aka ake yi a ginin, ya kuma ce, rushewar ginin abun takaici ne da suka wayi gari da shi.

  • FIFA Ta Fara Bincike Kan Sumbata Da Rubiales Ya Yi Wa ‘Yar Wasan Spain
  • Xi Jinping: Za Kara Karfin Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Ya ce: “Ba abun da muka tsammaci faruwarsa ba ne. Bar na yaba wa hukumomi, musamman NEMA da FEMA bisa kasancewa da suka yi a nan domin taimakonmu wajen ceton rayuwa a kalla 32. Abun bakin ciki da takaici mun rasa mutum biyu daga cikinsu.

“Ina fatan babban sakatare zai tabbatar an samar da kudaden da za a biya jinyar wadanda aka ceto, don kar mu sake rasa wani mutum kuma, sannan, wannan zai faru ne cikin gaggawa.

“Na biyu, wadannan abubuwan ne fa muke ta fada, ba wanda ya san hakan zai faru, kazalika, lokacin da gwamnati ta ce za ta dauki mataki kan gine-ginen da aka yi ba bisa ka’ida ba, ba za a yi hakan don wani mutum daya ko don ni ba ne, a’a za a yi ne don mu dukka kuma don komai su tafi daidai,” ya shaida.

Labarai Masu Nasaba

Lakurawa Sun Sanya Dokar Hana Sayar Da Shanu A Kebbi

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

Ministan FCT din ya nuna bacin ransa kan yadda hukumar kula da birnin tarayya (FCTA) ta dauki tsawon lokaci ba tare da ta zauna da mazauna kauyen Garki ba, ya ce, cikin gaggawa ya na son a zauna da mutanen kauyen domin fito musu da tsarin da gwamnati take son yi a wannan yankin.

“Idan gwamnati ta ce ga tsarin gini kaza da take son a yi, ba wai don a musguna ma wani ba ne, sam, illa domin a kare lafiyar kowa da kowa ne. An shirya birane domin dakile faruwar irin wannan. Abun takaici ka ga gine-gine ba tare da amincewar yin ginin ba. Na umarci a nemo tare kamo mamallakin wannan gini. Ya na da matukar muhimmanci.

“Babu shakka gwamnati za ta amshi ragamar wannan yankin kuma a tabbatar ba abun da ya sake faruwa. Ina rokon dukkanin mutanen wannan yankin da su ba mu hadin kai domin kyautata rayuwar kowa. Babu wanda ya zo nan domin ya ce ina son wane, ba na son wa ne.”

Daga karshe dai ya jajanta ma iyalan wadanda suka rasa rayukansu tare da addu’ar Allah zai bai wa wadanda suka jikkata lafiya.

Shi ma da yake jawabi, daraktan sanya ido kan harkokin bunkasawa ta hukumar FCTA, Muktar Galadima, ya ce za su cigaba da sanya ido domin tabbatar da jama’a su tashi a wuraren da ba amince a yi gini a cikinsu ba musamman wuraren da suke kan hanyar ruwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

FIFA Ta Fara Bincike Kan Sumbata Da Rubiales Ya Yi Wa ‘Yar Wasan Spain

Next Post

Xi Ya Yi Nuni Ga Ikon BRICS Na Juya Akalar Harkokin Duniya Zuwa Hanya Mai Bullewa

Related

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama
Manyan Labarai

Lakurawa Sun Sanya Dokar Hana Sayar Da Shanu A Kebbi

2 hours ago
Kawayen amarya
Manyan Labarai

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

10 hours ago
Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi
Labarai

Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

11 hours ago
Mutane Hudu Sun Mutu, An Ceto Wasu A Hatsarin Kwalekwale A Yauri
Labarai

Mutane Hudu Sun Mutu, An Ceto Wasu A Hatsarin Kwalekwale A Yauri

14 hours ago
EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana
Manyan Labarai

EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana

15 hours ago
Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo
Labarai

Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo

16 hours ago
Next Post
Xi Ya Yi Nuni Ga Ikon BRICS Na Juya Akalar Harkokin Duniya Zuwa Hanya Mai Bullewa

Xi Ya Yi Nuni Ga Ikon BRICS Na Juya Akalar Harkokin Duniya Zuwa Hanya Mai Bullewa

LABARAI MASU NASABA

Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka

Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka

June 19, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama

Lakurawa Sun Sanya Dokar Hana Sayar Da Shanu A Kebbi

June 19, 2025
Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

June 18, 2025
Kawayen amarya

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

June 18, 2025
Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

June 18, 2025
WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

June 18, 2025
Dan Wasan Gaban Chelsea, Murdyk Ka Iya Shafe Shekaru 4 Ba Tare Da Ya Buga Wasa Ba

Dan Wasan Gaban Chelsea, Murdyk Ka Iya Shafe Shekaru 4 Ba Tare Da Ya Buga Wasa Ba

June 18, 2025
Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

June 18, 2025
Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital

Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital

June 18, 2025
Mutane Hudu Sun Mutu, An Ceto Wasu A Hatsarin Kwalekwale A Yauri

Mutane Hudu Sun Mutu, An Ceto Wasu A Hatsarin Kwalekwale A Yauri

June 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.