ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rushewar Gini: Wike Ya Umarci A Cafko Mamallakin Ginin Cikin Gaggawa

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Wike

Biyo bayan rushewar wani gini mai hawa biyu a kan babban hanyar layin Legas da ke gundumar Garki II a Abuja wajajen karfe 11:45 na daren ranar Laraba, ministan birnin tarayya, Nyesom Wike, ya bada umarnin a gaggauta kamo wanda ya mallaki ginin da ya rushe din. 

Wike, wanda ya bada umarnin a lokacin da ya ziyarci wurin da lamarin ya faru da safiyar ranar Alhamis, ya jinjina da aikin ceto da aka ake yi a ginin, ya kuma ce, rushewar ginin abun takaici ne da suka wayi gari da shi.

  • FIFA Ta Fara Bincike Kan Sumbata Da Rubiales Ya Yi Wa ‘Yar Wasan Spain
  • Xi Jinping: Za Kara Karfin Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Ya ce: “Ba abun da muka tsammaci faruwarsa ba ne. Bar na yaba wa hukumomi, musamman NEMA da FEMA bisa kasancewa da suka yi a nan domin taimakonmu wajen ceton rayuwa a kalla 32. Abun bakin ciki da takaici mun rasa mutum biyu daga cikinsu.

ADVERTISEMENT

“Ina fatan babban sakatare zai tabbatar an samar da kudaden da za a biya jinyar wadanda aka ceto, don kar mu sake rasa wani mutum kuma, sannan, wannan zai faru ne cikin gaggawa.

“Na biyu, wadannan abubuwan ne fa muke ta fada, ba wanda ya san hakan zai faru, kazalika, lokacin da gwamnati ta ce za ta dauki mataki kan gine-ginen da aka yi ba bisa ka’ida ba, ba za a yi hakan don wani mutum daya ko don ni ba ne, a’a za a yi ne don mu dukka kuma don komai su tafi daidai,” ya shaida.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Ministan FCT din ya nuna bacin ransa kan yadda hukumar kula da birnin tarayya (FCTA) ta dauki tsawon lokaci ba tare da ta zauna da mazauna kauyen Garki ba, ya ce, cikin gaggawa ya na son a zauna da mutanen kauyen domin fito musu da tsarin da gwamnati take son yi a wannan yankin.

“Idan gwamnati ta ce ga tsarin gini kaza da take son a yi, ba wai don a musguna ma wani ba ne, sam, illa domin a kare lafiyar kowa da kowa ne. An shirya birane domin dakile faruwar irin wannan. Abun takaici ka ga gine-gine ba tare da amincewar yin ginin ba. Na umarci a nemo tare kamo mamallakin wannan gini. Ya na da matukar muhimmanci.

“Babu shakka gwamnati za ta amshi ragamar wannan yankin kuma a tabbatar ba abun da ya sake faruwa. Ina rokon dukkanin mutanen wannan yankin da su ba mu hadin kai domin kyautata rayuwar kowa. Babu wanda ya zo nan domin ya ce ina son wane, ba na son wa ne.”

Daga karshe dai ya jajanta ma iyalan wadanda suka rasa rayukansu tare da addu’ar Allah zai bai wa wadanda suka jikkata lafiya.

Shi ma da yake jawabi, daraktan sanya ido kan harkokin bunkasawa ta hukumar FCTA, Muktar Galadima, ya ce za su cigaba da sanya ido domin tabbatar da jama’a su tashi a wuraren da ba amince a yi gini a cikinsu ba musamman wuraren da suke kan hanyar ruwa.

Wike
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
Xi Ya Yi Nuni Ga Ikon BRICS Na Juya Akalar Harkokin Duniya Zuwa Hanya Mai Bullewa

Xi Ya Yi Nuni Ga Ikon BRICS Na Juya Akalar Harkokin Duniya Zuwa Hanya Mai Bullewa

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.