• English
  • Business News
Thursday, June 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ban Janye Wa Kowa Takara Ta Ba A Kaduna -Dan Takarar Gwamnan LP

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Ban Janye Wa Kowa Takara Ta Ba A Kaduna -Dan Takarar Gwamnan LP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar gwamna na jam’iyyar LP a Jihar Kaduna, Mista Jonathan Asake, ya ce bai janye wa kowa takararsa ba a zaben gwamnan da za a yi ranar Asabar.

Asake, ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Kafanchan, hedikwatar Karamar Hukumar Jema’a ta jihar.

  • ‘Yansanda Sun Cafke Mataimakin Shugaban APC Na Jihar Edo
  • DSS Ce Abokiyar Hamayyar Mu A Jihar Kano Ba APC Ba – NNPP

A cewarsa, zargin cewa ya karbi Naira miliyan 100 daga hannun Uba Sani, dan takarar gwamnan APC, da Gwamna Nasir el-Rufai don hada kai wajen kayar da PDP a ranar Asabar a matsayin labari mara tushe.

“Suna sanya guba a zukatan mutane cewa Uba Sani ne ke daukar nauyina domin a raba kuri’un Kudancin Kaduna, don Uba Sani ya yi nasara.

“Babu wani daga cikin shugabannin jam’iyyar PDP da zai iya fuskanta ta ya nemi na hakura da takarara, a maimakon haka sai suka koma yin amfani da ‘yan takara don ganin na sauka daga takara,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

Ya kalubalanci jam’iyyar PDP ko kuma duk wanda ke da shaidar cewa ya karbi kudin da ya bayyana su a bainar jama’a.

Dan takarar jam’iyyar LP ya ce a matsayinsa na daya daga cikin manyan masu sukar gwamnatin APC a jihar, ba zai taba shiga wata yarjejeniya ta siyasa da Uba Sani ko El-Rufai ba.

“Suna so su gamsar da masu zabe cewa kuri’ar jam’iyyar LP kuri’a ce ta APC.

“Duk wadannan labarun karya ne. Ban taba zama ba kuma ba zan taba zama da Uba Sani da Nasir El-Rufai kan kowace irin yarjejeniya ta siyasa ba.

“Ina kalubalantar kowa da ya zo da wata kwakkwarar shaidar da muka taba haduwa inda na karbi kudi a wurinsu,” in ji shi.

Asake ya yi alkawarin samar da ingantaccen shugabanci kuma abin koyi ga al’ummar Jihar Kaduna idan aka zabe shi a ranar Asabar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AsakeKadunaLPtakaraUba Sani
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Cafke Mataimakin Shugaban APC Na Jihar Edo

Next Post

Gwamnatin Osun Ta Ayyana Ranar Juma’a A Matsayin Hutu Saboda Zabe

Related

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano
Manyan Labarai

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

4 hours ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

6 hours ago
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato
Manyan Labarai

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

10 hours ago
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

14 hours ago
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno
Manyan Labarai

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

17 hours ago
Sanusi
Manyan Labarai

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

1 day ago
Next Post
Gwamnatin Osun Ta Ayyana Ranar Juma’a A Matsayin Hutu Saboda Zabe

Gwamnatin Osun Ta Ayyana Ranar Juma'a A Matsayin Hutu Saboda Zabe

LABARAI MASU NASABA

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

June 4, 2025
Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

June 4, 2025
Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

June 4, 2025
Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

June 4, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

June 4, 2025
Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

June 4, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

June 4, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

June 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.