ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ban Janye Wa Kowa Takara Ta Ba A Kaduna -Dan Takarar Gwamnan LP

by Sadiq
3 years ago
LP

Dan takarar gwamna na jam’iyyar LP a Jihar Kaduna, Mista Jonathan Asake, ya ce bai janye wa kowa takararsa ba a zaben gwamnan da za a yi ranar Asabar.

Asake, ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Kafanchan, hedikwatar Karamar Hukumar Jema’a ta jihar.

  • ‘Yansanda Sun Cafke Mataimakin Shugaban APC Na Jihar Edo
  • DSS Ce Abokiyar Hamayyar Mu A Jihar Kano Ba APC Ba – NNPP

A cewarsa, zargin cewa ya karbi Naira miliyan 100 daga hannun Uba Sani, dan takarar gwamnan APC, da Gwamna Nasir el-Rufai don hada kai wajen kayar da PDP a ranar Asabar a matsayin labari mara tushe.

ADVERTISEMENT

“Suna sanya guba a zukatan mutane cewa Uba Sani ne ke daukar nauyina domin a raba kuri’un Kudancin Kaduna, don Uba Sani ya yi nasara.

“Babu wani daga cikin shugabannin jam’iyyar PDP da zai iya fuskanta ta ya nemi na hakura da takarara, a maimakon haka sai suka koma yin amfani da ‘yan takara don ganin na sauka daga takara,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

Ya kalubalanci jam’iyyar PDP ko kuma duk wanda ke da shaidar cewa ya karbi kudin da ya bayyana su a bainar jama’a.

Dan takarar jam’iyyar LP ya ce a matsayinsa na daya daga cikin manyan masu sukar gwamnatin APC a jihar, ba zai taba shiga wata yarjejeniya ta siyasa da Uba Sani ko El-Rufai ba.

“Suna so su gamsar da masu zabe cewa kuri’ar jam’iyyar LP kuri’a ce ta APC.

“Duk wadannan labarun karya ne. Ban taba zama ba kuma ba zan taba zama da Uba Sani da Nasir El-Rufai kan kowace irin yarjejeniya ta siyasa ba.

“Ina kalubalantar kowa da ya zo da wata kwakkwarar shaidar da muka taba haduwa inda na karbi kudi a wurinsu,” in ji shi.

Asake ya yi alkawarin samar da ingantaccen shugabanci kuma abin koyi ga al’ummar Jihar Kaduna idan aka zabe shi a ranar Asabar.

MASU ALAKA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Next Post
Gwamnatin Osun Ta Ayyana Ranar Juma’a A Matsayin Hutu Saboda Zabe

Gwamnatin Osun Ta Ayyana Ranar Juma'a A Matsayin Hutu Saboda Zabe

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.