• English
  • Business News
Wednesday, August 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ban Nemi Kowa Don A Ba Ni Sarauta Ba – Aleiro 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Ban Nemi Kowa Don A Ba Ni Sarauta Ba – Aleiro 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ado Aleiro, dan bindigar da ya addabi jihar Zamfara da Katsina, wanda aka nada a matsayin Sarkin Fulani a Zamfara, ya ce babu wanda ya nema don yi masa sarautar.

Aleiro ya bayyana haka ne a wata hira da ya yi da DW Hausa kuma ta wallafa a ranar Lahadi.

  • Da Dumi-Dumi: ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3, Sun Sace Matafiya Da Dama A Katsina
  • Jami’an Tsaro Sun Kashe Mahara 2 A Anambra, Sun Kwato Makamai 

A ranar 16 ga watan Yuli ne Sarkin Yandoto, Aliyu Marafa, ya nada Aleiro a matsayin Sarkin Fulani a karamar hukumar Tsafe ta jihar.

Sai dai rundunar ‘yan sanda ta ce Aleiro na cikin jerin sunayen kasurguman da ake nema ruwa a jallo bisa zarginsa da hannu ra cikin ayyukan ‘yan bindiga.

Nadin sarauta ya janyo takadda sosai, hakan ya sa gwamnan Zamfara, Bello Matawalle, ya dakatar da sarkin ‘Yantodo saboda bai wa Aleiro sarauta.

Labarai Masu Nasaba

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

Remi Tinubu Ta Bada Gudunmawar Naira Biliyan 1 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwan Neja Ta Shafa

Matawalle ya kuma haramta wa sarakunan gargajiya a jihar bayar da mukaman sarauta ba tare da samun amincewar gwamnatin jihar ba.

Da yake mayar da martani kan nadin sarautar, Aleiro, ya ce masarautar ce ta neme shi da kanta.

“Bari in fada muku gaskiya, ba ni na nema ba; su suka neme ni game da hakan,” in ji Aleiro.

“Sun yi waya sun sanar da ni abin da za su ba ni. Sai na ce ‘a’a, wannan bai kamata ya faru ba.

“Amma da yake ina da iyaye, daga baya muka zauna muka tattauna a kai, kuma tun da sabon sarki ya fadi abin da yake son yi a masarautarsa, sai na amince.”

Ya kuma musanta cewa yana da hannu a wani harin da aka danganta da shi a kauyen Kadisau da ke karamar hukumar Faskari ta jihar Katsina, wanda ya faru a watan Yuni kuma aka kashe sama da mutane 30.

“Maganar Kadisau, don Allah, ina rokonka da sunan Allah da ka tambayi Sarkin Kadisau ko kuma ka nemi lambarsa ka tambaye shi musabbabin harin,” in ji shi.

“An yanka ‘yan uwanmu ne a cikin wani masallaci a ranar Juma’a a garin Kadisau. Abin da ya jawo harin kuma ‘yan uwansu ne suka dauki fansa. Ban san lokacin da harin ya faru ba; amma an alakanta ni da harin.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YantodoAdo AleiroFaskariHariKasurgumin Dan BindigaKatsinaSarautaSarkin Fulanin 'YandotoTsafeZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Dumi-Dumi: ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3, Sun Sace Matafiya Da Dama A Katsina

Next Post

Tsokaci A Kan Mazan Da Ba Su Barin Matansu Su Fita Aiki

Related

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

9 hours ago
Remi Tinubu Ta Bada Gudunmawar Naira Biliyan 1 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwan Neja Ta Shafa
Manyan Labarai

Remi Tinubu Ta Bada Gudunmawar Naira Biliyan 1 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwan Neja Ta Shafa

16 hours ago
Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32
Manyan Labarai

Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32

17 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

24 hours ago
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

2 days ago
Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 
Manyan Labarai

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

2 days ago
Next Post
Tsokaci A Kan Mazan Da Ba Su Barin Matansu Su Fita Aiki

Tsokaci A Kan Mazan Da Ba Su Barin Matansu Su Fita Aiki

LABARAI MASU NASABA

Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

August 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

August 6, 2025
Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

August 6, 2025
Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

August 5, 2025
Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

August 5, 2025
Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

August 5, 2025
Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

August 5, 2025
Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

August 5, 2025
Sin Ta Fitar Da Shirin Kyautata Muhalli Domin Inganta Kiwon Lafiya Na Shekaru Biyar

Sin Ta Fitar Da Shirin Kyautata Muhalli Domin Inganta Kiwon Lafiya Na Shekaru Biyar

August 5, 2025
Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina

Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina

August 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.