• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ban Nemi Kowa Don A Ba Ni Sarauta Ba – Aleiro 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Ban Nemi Kowa Don A Ba Ni Sarauta Ba – Aleiro 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ado Aleiro, dan bindigar da ya addabi jihar Zamfara da Katsina, wanda aka nada a matsayin Sarkin Fulani a Zamfara, ya ce babu wanda ya nema don yi masa sarautar.

Aleiro ya bayyana haka ne a wata hira da ya yi da DW Hausa kuma ta wallafa a ranar Lahadi.

  • Da Dumi-Dumi: ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3, Sun Sace Matafiya Da Dama A Katsina
  • Jami’an Tsaro Sun Kashe Mahara 2 A Anambra, Sun Kwato Makamai 

A ranar 16 ga watan Yuli ne Sarkin Yandoto, Aliyu Marafa, ya nada Aleiro a matsayin Sarkin Fulani a karamar hukumar Tsafe ta jihar.

Sai dai rundunar ‘yan sanda ta ce Aleiro na cikin jerin sunayen kasurguman da ake nema ruwa a jallo bisa zarginsa da hannu ra cikin ayyukan ‘yan bindiga.

Nadin sarauta ya janyo takadda sosai, hakan ya sa gwamnan Zamfara, Bello Matawalle, ya dakatar da sarkin ‘Yantodo saboda bai wa Aleiro sarauta.

Labarai Masu Nasaba

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

Matawalle ya kuma haramta wa sarakunan gargajiya a jihar bayar da mukaman sarauta ba tare da samun amincewar gwamnatin jihar ba.

Da yake mayar da martani kan nadin sarautar, Aleiro, ya ce masarautar ce ta neme shi da kanta.

“Bari in fada muku gaskiya, ba ni na nema ba; su suka neme ni game da hakan,” in ji Aleiro.

“Sun yi waya sun sanar da ni abin da za su ba ni. Sai na ce ‘a’a, wannan bai kamata ya faru ba.

“Amma da yake ina da iyaye, daga baya muka zauna muka tattauna a kai, kuma tun da sabon sarki ya fadi abin da yake son yi a masarautarsa, sai na amince.”

Ya kuma musanta cewa yana da hannu a wani harin da aka danganta da shi a kauyen Kadisau da ke karamar hukumar Faskari ta jihar Katsina, wanda ya faru a watan Yuni kuma aka kashe sama da mutane 30.

“Maganar Kadisau, don Allah, ina rokonka da sunan Allah da ka tambayi Sarkin Kadisau ko kuma ka nemi lambarsa ka tambaye shi musabbabin harin,” in ji shi.

“An yanka ‘yan uwanmu ne a cikin wani masallaci a ranar Juma’a a garin Kadisau. Abin da ya jawo harin kuma ‘yan uwansu ne suka dauki fansa. Ban san lokacin da harin ya faru ba; amma an alakanta ni da harin.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YantodoAdo AleiroFaskariHariKasurgumin Dan BindigaKatsinaSarautaSarkin Fulanin 'YandotoTsafeZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Dumi-Dumi: ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3, Sun Sace Matafiya Da Dama A Katsina

Next Post

Tsokaci A Kan Mazan Da Ba Su Barin Matansu Su Fita Aiki

Related

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

9 hours ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

11 hours ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

11 hours ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

1 day ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

1 day ago
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja
Manyan Labarai

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

1 day ago
Next Post
Tsokaci A Kan Mazan Da Ba Su Barin Matansu Su Fita Aiki

Tsokaci A Kan Mazan Da Ba Su Barin Matansu Su Fita Aiki

LABARAI MASU NASABA

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

June 6, 2025
Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

June 6, 2025
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

June 6, 2025
aure

Kar Ki Bari Naman Sallah Ya Kashe Miki Aure Yar’uwa

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.