ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ban Nemi Kowa Don A Ba Ni Sarauta Ba – Aleiro 

by Sadiq
4 years ago
Aleiro

Ado Aleiro, dan bindigar da ya addabi jihar Zamfara da Katsina, wanda aka nada a matsayin Sarkin Fulani a Zamfara, ya ce babu wanda ya nema don yi masa sarautar.

Aleiro ya bayyana haka ne a wata hira da ya yi da DW Hausa kuma ta wallafa a ranar Lahadi.

  • Da Dumi-Dumi: ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3, Sun Sace Matafiya Da Dama A Katsina
  • Jami’an Tsaro Sun Kashe Mahara 2 A Anambra, Sun Kwato Makamai 

A ranar 16 ga watan Yuli ne Sarkin Yandoto, Aliyu Marafa, ya nada Aleiro a matsayin Sarkin Fulani a karamar hukumar Tsafe ta jihar.

ADVERTISEMENT

Sai dai rundunar ‘yan sanda ta ce Aleiro na cikin jerin sunayen kasurguman da ake nema ruwa a jallo bisa zarginsa da hannu ra cikin ayyukan ‘yan bindiga.

Nadin sarauta ya janyo takadda sosai, hakan ya sa gwamnan Zamfara, Bello Matawalle, ya dakatar da sarkin ‘Yantodo saboda bai wa Aleiro sarauta.

LABARAI MASU NASABA

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa

Matawalle ya kuma haramta wa sarakunan gargajiya a jihar bayar da mukaman sarauta ba tare da samun amincewar gwamnatin jihar ba.

Da yake mayar da martani kan nadin sarautar, Aleiro, ya ce masarautar ce ta neme shi da kanta.

“Bari in fada muku gaskiya, ba ni na nema ba; su suka neme ni game da hakan,” in ji Aleiro.

“Sun yi waya sun sanar da ni abin da za su ba ni. Sai na ce ‘a’a, wannan bai kamata ya faru ba.

“Amma da yake ina da iyaye, daga baya muka zauna muka tattauna a kai, kuma tun da sabon sarki ya fadi abin da yake son yi a masarautarsa, sai na amince.”

Ya kuma musanta cewa yana da hannu a wani harin da aka danganta da shi a kauyen Kadisau da ke karamar hukumar Faskari ta jihar Katsina, wanda ya faru a watan Yuni kuma aka kashe sama da mutane 30.

“Maganar Kadisau, don Allah, ina rokonka da sunan Allah da ka tambayi Sarkin Kadisau ko kuma ka nemi lambarsa ka tambaye shi musabbabin harin,” in ji shi.

“An yanka ‘yan uwanmu ne a cikin wani masallaci a ranar Juma’a a garin Kadisau. Abin da ya jawo harin kuma ‘yan uwansu ne suka dauki fansa. Ban san lokacin da harin ya faru ba; amma an alakanta ni da harin.”

MASU ALAKA

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta
Manyan Labarai

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

June 26, 2026
Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa
Manyan Labarai

Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa

June 26, 2026
Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila
Manyan Labarai

Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila

June 26, 2026
Next Post
Tsokaci A Kan Mazan Da Ba Su Barin Matansu Su Fita Aiki

Tsokaci A Kan Mazan Da Ba Su Barin Matansu Su Fita Aiki

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

June 26, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A  Titin Bypass

Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A Titin Bypass

June 26, 2026
Disu

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

June 26, 2026
Aleiro

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Fara Aikin Gina Mayankar Zamani A Garin Jos

June 26, 2026
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

June 26, 2026
NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

June 26, 2026
An Fitar da Jadawalin Wasannin Zagayen Farko Na Gasar Carabao Cup ta 2026/2027

An Fitar da Jadawalin Wasannin Zagayen Farko Na Gasar Carabao Cup ta 2026/2027

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ba Ta Da Hujjar Umartar INEC Ta Soke Rajistar Jam’iyyu —Uban Doman Lafiya

June 26, 2026
Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

June 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.