ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ban Nemi Kowa Don A Ba Ni Sarauta Ba – Aleiro 

by Sadiq
4 years ago
Aleiro

Ado Aleiro, dan bindigar da ya addabi jihar Zamfara da Katsina, wanda aka nada a matsayin Sarkin Fulani a Zamfara, ya ce babu wanda ya nema don yi masa sarautar.

Aleiro ya bayyana haka ne a wata hira da ya yi da DW Hausa kuma ta wallafa a ranar Lahadi.

  • Da Dumi-Dumi: ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3, Sun Sace Matafiya Da Dama A Katsina
  • Jami’an Tsaro Sun Kashe Mahara 2 A Anambra, Sun Kwato Makamai 

A ranar 16 ga watan Yuli ne Sarkin Yandoto, Aliyu Marafa, ya nada Aleiro a matsayin Sarkin Fulani a karamar hukumar Tsafe ta jihar.

ADVERTISEMENT

Sai dai rundunar ‘yan sanda ta ce Aleiro na cikin jerin sunayen kasurguman da ake nema ruwa a jallo bisa zarginsa da hannu ra cikin ayyukan ‘yan bindiga.

Nadin sarauta ya janyo takadda sosai, hakan ya sa gwamnan Zamfara, Bello Matawalle, ya dakatar da sarkin ‘Yantodo saboda bai wa Aleiro sarauta.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

Matawalle ya kuma haramta wa sarakunan gargajiya a jihar bayar da mukaman sarauta ba tare da samun amincewar gwamnatin jihar ba.

Da yake mayar da martani kan nadin sarautar, Aleiro, ya ce masarautar ce ta neme shi da kanta.

“Bari in fada muku gaskiya, ba ni na nema ba; su suka neme ni game da hakan,” in ji Aleiro.

“Sun yi waya sun sanar da ni abin da za su ba ni. Sai na ce ‘a’a, wannan bai kamata ya faru ba.

“Amma da yake ina da iyaye, daga baya muka zauna muka tattauna a kai, kuma tun da sabon sarki ya fadi abin da yake son yi a masarautarsa, sai na amince.”

Ya kuma musanta cewa yana da hannu a wani harin da aka danganta da shi a kauyen Kadisau da ke karamar hukumar Faskari ta jihar Katsina, wanda ya faru a watan Yuni kuma aka kashe sama da mutane 30.

“Maganar Kadisau, don Allah, ina rokonka da sunan Allah da ka tambayi Sarkin Kadisau ko kuma ka nemi lambarsa ka tambaye shi musabbabin harin,” in ji shi.

“An yanka ‘yan uwanmu ne a cikin wani masallaci a ranar Juma’a a garin Kadisau. Abin da ya jawo harin kuma ‘yan uwansu ne suka dauki fansa. Ban san lokacin da harin ya faru ba; amma an alakanta ni da harin.”

MASU ALAKA

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna
Rahotonni

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

July 18, 2026
Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah
Manyan Labarai

Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

July 18, 2026
Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Next Post
Tsokaci A Kan Mazan Da Ba Su Barin Matansu Su Fita Aiki

Tsokaci A Kan Mazan Da Ba Su Barin Matansu Su Fita Aiki

LABARAI MASU NASABA

Kura-kurai 7 Da Mata Ke Yi Wajen Kula Da Fatarsu

Kura-kurai 7 Da Mata Ke Yi Wajen Kula Da Fatarsu

July 18, 2026
Majalisa Ta Goyi Bayan CBN Kan Sauya Fasalin Naira Bayan Tafka Muhawara 

Majalisa Ta Yi Watsi Da Bukatar MDD Ta Bincikar Badakalar Satar Daliban Oyo

July 18, 2026
Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

July 18, 2026
Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

July 18, 2026
Tasirin Da VAR Ta Yi A Gasar Kofin Duniya

Tasirin Da VAR Ta Yi A Gasar Kofin Duniya

July 18, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.