Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

An Bankaɗo Badaƙala A Hukumar Kula Da Malanta Ta Bauchi

by Tayo Adelaja
October 12, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Khalid Idris Doya, Bauchi

Majalisar Dokokin jihar Bauchi ta gayyaci shuwagabanin hukumar da ke kula da malamai ta jihar Bauchi ‘Teachers Service Commission’ don su bayyana a gabanta don yin bada bahasi kan saida takardun ɗaukan aikin koyarwa da ke gudana a halin yanzu a kan kuɗi naira ɗari biyar a maimakon ɗaya ɗaya kacal.

samndaads

Mamba mai wakiltar mazaɓar Dass Maryam Garba Ɓagel itace ta kawo ƙudirin a gaban majalisar ta ce hukumar da ke kula da malamai na jihar Bauchi ta saida takardar guraben aiki a kan naira dari biyar 500 a maimakon naira 100 kacal da suka sayar a kwanakin baya, inda take cewa “Hukumar ɗaukan malamai ta saida fom wajen guda dubu biyar 5,000 a kan kuɗi har naira 500 wanda kuma fom ɗin nan a naira 100 ake saida shi”.

A bisa haka ne ta buƙaci majalisar ta gayatoci shuwagabanin TSC domin su bada bahasi kan wannan lamarin. Wakilinmu ya nemi jin ta bakin shugaban hukumar kula da malamai ta jihar Bauchi M.N Fa’izu Saleh inda ya ƙi cewa uffan kan lamarin.

Haka zalika a yayin zaman mamba mai wakiltar Azare/Maɗangala Tijjani Muhammadu Aliyu ya buƙaci gwamnatin jiha da ta gyara asibitin Azare “Da yawan asibitocinmu za ka lura suna cikin wani hali wanda babu kyan gani”.

Ya ce babban asibitin garin na Azare ya riga ya gama lalacewar da har yana hana ma’aikatan yin aikinsu yanda ya kamata, a cewarsa ƙananan hukumomin da suke da makwafta da Azare na zuwa wannan asibitin a don haka da buƙatar a yi masa garan bawul. Da ya ke  jawabin goyon baya kan ƙudurin mamba mai wakiltar Katagum Ibrahim Bello ya yi ƙira ga gwamnati da ta sanya dokar ta ɓaci a sashin lafiya da ke jihar domin samun gyarar da ta dace.

SendShareTweetShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Daɗi Sun Kashe Tsohon Shugaban Ma’aikatan Filato

Next Post

Farashin Shinkafar Gida Ya Faɗi

RelatedPosts

Neja

Tsaro; Sakataren Gwamnatin Neja Ya Nemi ‘Yan Bindiga Su Aje Makamai

by Muhammad
5 days ago
0

Daga Muhammad Awwal Umar, Sakataren gwamnatin Neja, Ahmed Ibrahim Matane...

Tinubu

Sanata Tinubu Ya Bukaci A Kara Samar Da Zaman Lafiya Tsakanin Al’umma

by Muhammad
5 days ago
0

Daga Idris Aliyu Daudawa, Jagoran jam'iyyar babbar jam’iyya mai mulkin...

Miyagun Kwayoyi

Shugaban NDLEA Ya Yi Alkawarin Fattatakar Dillalan Miyagun Kwaya A Nijeriya

by Muhammad
5 days ago
0

Daga Bello Hamza, Shugaban hukumar NDLEA, Brig. Gen. Buba Marwa...

Next Post

Farashin Shinkafar Gida Ya Faɗi

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version