• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bankwana Da 2023: Radadin Cire Tallafin Mai

by Bello Hamza
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Bankwana Da 2023: Radadin Cire Tallafin Mai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Ranar 29 ga watan Mayun 2023, da aka rantsar da Asiwaju Bola Tinubu a matsayin Shugaban Nijeriya na 16, za ta ci gaba da kasancewa a cikin tarihi bisa yadda sanarwar da sabon shugaban ya yi na cire tallafin mai za ta ci gaba da kai-komo a zukatan ‘Yan Nijeriya musamman wadanda ke matukar jin radadin abin.

Duk da yake Tinubu ya yi bayanin cewa zai cire tallafin tun a lokacin da yake yakin neman zabe, amma kuma abin ya zo da ba-zata. Kasancewar man fetur ya shafi kusan dukkan bangarorin rayuwar al’umma, nan take aka fuskanci tsadar rayuwa tun daga farashin sufuri da hauhawar farashin kayan masarufi, wanda hakan ya jefa al’ummar Nijeriya cikin halin ni-‘yasu.

  • Tinubu Ya Yi Allah-Wadai Da Harin ‘Yan Ta’adda A Filato
  • Boss Mustapha Ya Karyata Zargin Satar Dala Miliyan 6.3 Daga CBN

Lokacin da Tinubu ya sanar da cire tallafin gaba daya, dokar alkinta albarkatun man fetur ta (PIA) ta riga ta cire tallafin kusan wata 15 da suka gabata amma gwamnatin Shugaba Buhari ta san dabarar da ta shigar da Naira Tiriliyan 3.36 cikin kasafin kudin shekarar 2022 don ta tsawaita lamarin tallafin zuwa watan Yuni na shekarar 2023.

Kungiyar kwadago ta kasa NLC ta bayyana rashin jin dadinta da janye tallafin man, inda ta yi korafin cewa ya kamata gwamnati ta fadada tattaunawa da masu ruwa da tsaki tare da fito da tsare-tsaren da za su rage wa al’umma radadin da janye tallafin zai haifar a rayuwar yau da kullum, ta kuma yi barazanar tsuduma yajin aiki in har gwamnati ba ta yi abin da ya kamata ba. Amma tattaunawar da bangaren gwamnati da shugabannin kungiyar suka yi ta haifar da fahimtar juna duk kuwa da wata kotun tarayya ta haramta wa kungiyar kwadagon shiga yajin aikin, kungiyar kwadagon ta janye yajin aikin da ta shirya shiga ranar Laraba 6 ga watan Yuni.

Don fahimtar halin da al’umma suka shiga sakamakon cire tallafin wani mai sharhi a kan al’amurran yau da kullum, Malam Bashir Dalhatu ya yi nazari da bibiyar rayuwar ‘yan uwa da abokan arziki, inda ya yi nazari halin da magidanci mai ‘ya’ya biyu ke ciki sakamakon cire tallafin man a Nijeriya.

Ya ba da misali da kudin da magidancin zai iya kashewa a abincin rana daya kamar haka: abincin safe, burodi =N600, kosai =N300, ruwan shayi ba madara= N200, ya kama= N1,100, a wata N1,100 sau 30 = N33,000. In kuma in zai yi wainar fulawa, ga yadda za ta kasance, fulawa= N400, Mai N250, Magi N100, kayan miya N50, koko N200, sukari N150, gawayi N100, ya kama: N1,250, kenan a wata, abin da za a kashe ya kama N1,250 sau 30 = N37,500 a cin abin safe kwai.

Abinci rana kuma an kiyasta zai kashe N29,100 a duk wata a abincin dare kuma zai iya kashe N21,900, in aka hada da kudin ruwan sha na N4500 duk wata zai kashe N88,500 kenan a duk wata idan zai sha shayi ba madara kuma ba zai ci abinci da kifi ko nama ba. Idan kuma wainar fulawa zai yi da safe zai kashe N93,000 a wata shi ma dai ban da kifi da nama.

Wannan lissafin na magidanci ne mai ‘ya’ya biyu kuma ba a saka kudin haya, kudin wuta, rashin lafiya, kudin zuwa aiki, omo, sabulu da sauran su.

Idan aka lura da mafi karancin albashi na N30,000 ga ma’aikatan Nijeriya wanda ma har zuwa yanzu wasu jihohi da kananan hukumomi ba su fara aiwatar da biyan albashin ba, tabbas magidanta a Nijeriya sun shiga halin matsi sosai.

Haka kuma ba a hada da kudin makarantar boko na yara, da kudin makarantar islamiyya da na kayan sawa ba wanda dukkan su cire tallafin mai ya shafe su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bankwana Da 2023: Wasu Abubuwan Da Suka Dauki Hankali A Fannin Tsaro

Next Post

Bankwana Da 2023: Tirka-tirkar Canjin Kudi

Related

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Manyan Labarai

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

8 hours ago
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

20 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

22 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

2 days ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

2 days ago
NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja
Manyan Labarai

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

2 days ago
Next Post
Bankwana Da 2023: Tirka-tirkar Canjin Kudi

Bankwana Da 2023: Tirka-tirkar Canjin Kudi

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

October 5, 2025
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

October 5, 2025
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

October 5, 2025
Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.