• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bankwana Da 2023: Radadin Cire Tallafin Mai

by Bello Hamza
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Bankwana Da 2023: Radadin Cire Tallafin Mai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

Ranar 29 ga watan Mayun 2023, da aka rantsar da Asiwaju Bola Tinubu a matsayin Shugaban Nijeriya na 16, za ta ci gaba da kasancewa a cikin tarihi bisa yadda sanarwar da sabon shugaban ya yi na cire tallafin mai za ta ci gaba da kai-komo a zukatan ‘Yan Nijeriya musamman wadanda ke matukar jin radadin abin.

Duk da yake Tinubu ya yi bayanin cewa zai cire tallafin tun a lokacin da yake yakin neman zabe, amma kuma abin ya zo da ba-zata. Kasancewar man fetur ya shafi kusan dukkan bangarorin rayuwar al’umma, nan take aka fuskanci tsadar rayuwa tun daga farashin sufuri da hauhawar farashin kayan masarufi, wanda hakan ya jefa al’ummar Nijeriya cikin halin ni-‘yasu.

  • Tinubu Ya Yi Allah-Wadai Da Harin ‘Yan Ta’adda A Filato
  • Boss Mustapha Ya Karyata Zargin Satar Dala Miliyan 6.3 Daga CBN

Lokacin da Tinubu ya sanar da cire tallafin gaba daya, dokar alkinta albarkatun man fetur ta (PIA) ta riga ta cire tallafin kusan wata 15 da suka gabata amma gwamnatin Shugaba Buhari ta san dabarar da ta shigar da Naira Tiriliyan 3.36 cikin kasafin kudin shekarar 2022 don ta tsawaita lamarin tallafin zuwa watan Yuni na shekarar 2023.

Kungiyar kwadago ta kasa NLC ta bayyana rashin jin dadinta da janye tallafin man, inda ta yi korafin cewa ya kamata gwamnati ta fadada tattaunawa da masu ruwa da tsaki tare da fito da tsare-tsaren da za su rage wa al’umma radadin da janye tallafin zai haifar a rayuwar yau da kullum, ta kuma yi barazanar tsuduma yajin aiki in har gwamnati ba ta yi abin da ya kamata ba. Amma tattaunawar da bangaren gwamnati da shugabannin kungiyar suka yi ta haifar da fahimtar juna duk kuwa da wata kotun tarayya ta haramta wa kungiyar kwadagon shiga yajin aikin, kungiyar kwadagon ta janye yajin aikin da ta shirya shiga ranar Laraba 6 ga watan Yuni.

Don fahimtar halin da al’umma suka shiga sakamakon cire tallafin wani mai sharhi a kan al’amurran yau da kullum, Malam Bashir Dalhatu ya yi nazari da bibiyar rayuwar ‘yan uwa da abokan arziki, inda ya yi nazari halin da magidanci mai ‘ya’ya biyu ke ciki sakamakon cire tallafin man a Nijeriya.

Ya ba da misali da kudin da magidancin zai iya kashewa a abincin rana daya kamar haka: abincin safe, burodi =N600, kosai =N300, ruwan shayi ba madara= N200, ya kama= N1,100, a wata N1,100 sau 30 = N33,000. In kuma in zai yi wainar fulawa, ga yadda za ta kasance, fulawa= N400, Mai N250, Magi N100, kayan miya N50, koko N200, sukari N150, gawayi N100, ya kama: N1,250, kenan a wata, abin da za a kashe ya kama N1,250 sau 30 = N37,500 a cin abin safe kwai.

Abinci rana kuma an kiyasta zai kashe N29,100 a duk wata a abincin dare kuma zai iya kashe N21,900, in aka hada da kudin ruwan sha na N4500 duk wata zai kashe N88,500 kenan a duk wata idan zai sha shayi ba madara kuma ba zai ci abinci da kifi ko nama ba. Idan kuma wainar fulawa zai yi da safe zai kashe N93,000 a wata shi ma dai ban da kifi da nama.

Wannan lissafin na magidanci ne mai ‘ya’ya biyu kuma ba a saka kudin haya, kudin wuta, rashin lafiya, kudin zuwa aiki, omo, sabulu da sauran su.

Idan aka lura da mafi karancin albashi na N30,000 ga ma’aikatan Nijeriya wanda ma har zuwa yanzu wasu jihohi da kananan hukumomi ba su fara aiwatar da biyan albashin ba, tabbas magidanta a Nijeriya sun shiga halin matsi sosai.

Haka kuma ba a hada da kudin makarantar boko na yara, da kudin makarantar islamiyya da na kayan sawa ba wanda dukkan su cire tallafin mai ya shafe su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bankwana Da 2023: Wasu Abubuwan Da Suka Dauki Hankali A Fannin Tsaro

Next Post

Bankwana Da 2023: Tirka-tirkar Canjin Kudi

Related

Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

8 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

10 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

13 hours ago
Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

19 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

1 day ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

2 days ago
Next Post
Bankwana Da 2023: Tirka-tirkar Canjin Kudi

Bankwana Da 2023: Tirka-tirkar Canjin Kudi

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.