ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bankwana Da 2023: Wasu Abubuwan Da Suka Dauki Hankali A Fannin Tsaro

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
2023

Nijeriya ta kwashe tsawon wasu shekaru tana fama da tabarbarewar tsaro wanda ya yi sanadiyyar salwantar rayukan jama’a da dukiyoyi da dama. Duk da cewa a 2022, tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya lashi takobin ba zai gadar wa shugaban kasa na gaba da matsalar tsaro ba, amma hakan bai hana matsalar ta tsaro ci gaba da addabar Nijeriya a 2023 ba, wanda gwamnatocin kasar ke ta fafatukar magancewa.

Tun daga farkon shekarar ta 2023 har zuwa karshenta da muke gani yanzu, akwai mayakan kasar da ke fafatawa da ‘yan ta’adda a karkashin shirye-shirye masu yawa na rundunonin tsaro.

  • Tinubu Ga Gwamnoni: Dole Ne Mu Tabbatar Da Zaman Lafiya A Nijeriya
  • An Wallafa Littafin Xi Jinping Game Da BRI Bugun Shekarar 2023

A farkon makon nan, babban hafsan mayakan kasa na Nijeriya, Lt. General Taoreed Lagbaja ya bayyana cewa akwai dakarun soji fiye da 50,000 da ke ayyukan tsaro daban-daban a sassan kasar nan.

ADVERTISEMENT

Wasu daga cikin ‘yan majalisar dattawan Nijeriya, sun bayyana cewar matukar ana son samun nasarar magance matsalolin ‘yan bindiga da sauran kalubalen tsaron da kasar ke fuskanta, sai an samu hadin kai a tsakanin hukumomin tsaro.

Kamar yadda aka yi tsammani, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ritayar da dukkan hafsoshin sojin kasar da sufeto-janar na ‘yansanda, da sauran masu ruwa da tsaki a harkar tsaro kamar mai ba da shawara kan tsaron kasa da wasu shugabannin hukomomin tsaro da ba na soja ba, wadanda ya gada daga tsohon shugaba Muhammadu Buhari.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Sabbin nade-naden sun zo da ba-zata inda aka jiyo sunan Mallam Nuhu Ribadu a matsayin Mai Ba wa Shugaban Kasar Shawara Kan Harkokin Tsaron Kasa, wanda kuma shi ne dansanda na farko da aka taba nadawa a wannan mukami a tarihin Nijeriya. Sai kuma Janar C.G Musa a matsayin Babban Hafsan Tsaro, yayin da, Laftanar Janar T. A Lagbaja ya zama Babban Hafsan Sojin Kasa. sai kuma Rear Admirral E. A Ogalla da aka nada Babban Hafsan Sojojin Ruwa.

Haka nan Tinubu ya nada, ABM H.B Abubakar Babban Hafsan Sojojin Sama, sai kuma Kayode Egbetokun a matsayin Sufeto-Janar na ‘Yansanda. Manjo Janar. EPA Undiandeye a matsayin Babban Hafsan Hukumar Tattara Bayanan Sirri na Soja.

Sabbin shugabannin tsaron da aka nada sun bayyana kudirinsu na fuskantar matsalar tsaron da Nijeriya ke kaka-ni-ka-yi a ciki. Sai dai duk da cewa akwai nasarori da suke samu amma kuma akwai sabbin kalubale da ke kunno kai, kamar dawowar hare-haren boko haram da sauya dabarun ‘yan bindiga da kuma tafka mugun kuskure na jefa wa fararen hula bam daga jami’an tsaro.

  • Dawowar ‘yan ta’addan Boko-Haram

Jama’a sun fara bayyana shakku dangane da yadda ake fuskantar barazanar dawowar hare-haren mayakan kungiyar Boko Haram a Jihohin Borno da Yobe, a daidai lokacin da ake tsammanin an raka bako; ashe yana labe a bayan gari.

Hakan ya biyo bayan wasu munanan hare-haren da mayakan ke ci gaba da aiwatarwa a wasu sassan jihohin biyu.

A shekarar ta 2023, akwai lokacin da cikin kasa da wata daya, mayakan suka aiwatar da munanan hare-haren da suka jawo salwantar rayuka sama da 50 a Borno, kana suka kashe kimanin 40 a Kauyen Nguro-kayya dake Karamar Hukumar Gaidam a Jihar Yobe. Ko a wannan makon da ake dab da bankwana da shekarar, sun tarwatsa wasu kayayyakin lantarki da suka yi sanadin jefa Borno da Yobe cikin duhu.

  • Yunkurin sulhu da ‘yan bindiga da ci gaba da tafka ta’asarsu

Shawarar da tsohon Gwamnan farar hula na farko a Jihar Zamfara, Sanata Ahmad Sani Yarima ya bayar na batun sulhu da ‘yan bindiga a yankin arewa maso yamma ya tayar da kura ainun a Nijeriya inda aka yi ta Allah wadai da lamarin.

Ana ganin matukar an yi sulhu da ‘yan bindigar zai zama duk ta’asar da suka yi sun ci bulus kenan. Amma duk da kushen sulhun, sai ga shi wata tawaga da ta tace ministocin tsaro ne daga Abuja suka aiko ta, a boye ta gana da ‘yan bindiga a yankin Katsina don sulhu. Daga bisani Gwamnatin Zamfara ta yi tutsu da lamarin inda ita ma Gwamnatin Katsina ta ce babu hannunta, suka kuma sake jaddada aniyarsu ta yakar ‘yan bindigar ta hanyar kafa dakarun tsaron garuruwa. Katsina ta riga ta kaddamar da nata, yayin da Zamfara ke dab da kamala horas da nata.

Wannan ya sa ‘yan bindigar sun ci gaba da tafka ta’asa a arewa maso yamma inda ko a cikin Disambar nan sun kashe mutane a Zurmi da tsakanin Jibiya da Katsina baya ga sauran kauyuka da suke sace mutane saboda sun ki biyan harajin da suka kakaba musu.

Daruruwan mutanen da ‘yan bindiga ke kashewa a da matukar tayar da hankali a Nijeriya musamman yadda ko a ranar Kirsimeti, suka farmaki wasu garuruwa akalla 15 a Jihar Filato inda rahotanni ke cewa an kashe akalla mutum 160 zuwa lokacin hada wannan rahoton.

  • Hare-haren sojoji a kan fararen hula

Harin da sojoji suka kai bisa kuskure kan farar hula da ke taron Mauludi a kauyen Tudun Biri da ke Jihar Kaduna, a ranar 3 ga Disamban 2023, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane akalla 85 ne ya fi daukar hankali a kan wadanda suka auku a baya a shekarar ta 2023.

Masana harkokin tsaro sun dade suna sukar irin sakacin da ake samu a yaki da ‘yan Boko Haram a Arewa maso Gabas da kuma na ‘yan bindiga a arewa maso yamma, da ke ritsawa da rayukan fararen hula wadanda ba su ji ba, ba su gani ba.

 A farkon wannan shekarar (ranar 25 ga watan Janairu 2023) an kashe mutum 40 sakamakon harin da jirgin yaki ya kai a kan fararen hula a Jihar Nasarawa, haka kuma a a ranar 5 ga watan Maris 2023 inda mutum uku suka mutu a harin da wani jigin yaki ya kai a kan mutane, daga nan kuma sai harin da jirgin saman sojoji ya kai a ranar 18 ga watan Agusta 2023 inda mutum daya ya mutu.

  • Nasarorin da jami’an tsaro suka samu

Shalkwatar rundunar tsaro ta sojin Nijeriya ta rika bayyana nasarorin da dakarunta suke samu na halaka daruruwan ‘yan ta’addar Boko Haram da kuma ‘yan bindiga a sassa daban-daban na kasar nan.

Har ila yau, sun bayar da rahotannin kwato makamai da sauran kayan abinci, babura, abubuwan fashewa shanu daga hannun ‘yan ta’addar. Haka nan sun kwato danyen Mai na sata da kuma Gas na mota wanda kudinsu ya kai Naira miliyan 259 daga hannun tsagerun yankin Neja Delta.

Bugu da kari, dakarun sojojin Nijeriya sun samu nasarar tarwatsa mafakar kasurguman ‘yan bindiga a jihohin Zamfara da Sokoto. Kakakin rundunar Operation Hadarin Daji, Kyaftin Yahaya Ibrahim, ya ce sojojin sun kara matsa kaimi a yakin da suke da ‘yan bindiga a shiyyar Arewa maso Yamma.

Ko a ranar Alhamis ta makon jiya, mai Magana da yawun shalkwatar tsaro ta Nijeriya, Manjo Janar Edward Buba ya ce cikin mako daya a watan Dismabar nan, sojoji sun kashe ‘yan ta’adda 40 da cafke 191 da kuma ceto mutum 80 da aka sace ana garkuwa da su. Haka nan su ma barayin mai akalla 68 sun shiga hannu.

Hakazalika, kashe kasurgumin dan bindigar nan da aka fi sani da Kachalla a arewa maso yamma wata manuniya ce ga irin nasarorin da jami’an tsaron ke samu.

Duk a shekarar ta 2023, sojojin sun kai samamen shara a kauyukan Dada, Rukudawa, da Dumburum duk a karamar hukumar Zurmi ta Jihar Zamfara. A cewarsa, yayin wannan samamen, sojoji sun yi musayar wuta da ‘yan bindiga suka nuna musu karfin sanin aiki wanda bisa tilas ‘yan ta’addar suka tsere da raunuka. Sannan dakarun sun hallaka dan bindiga daya a musayar wutar da suka yi.

Karin girma da ritaya

Duk dai a shekarar ta 2023, an yi wasu manyan sojoji akalla 115 ritaya yayin da aka kara wa wasu 214 girma ciki akwai manjo janar 122 da Birgediya Janar. Karin girman ya shafi dakarun ruwa da na sama.

2023
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Bankwana Da 2023: Radadin Cire Tallafin Mai

Bankwana Da 2023: Radadin Cire Tallafin Mai

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.