• English
  • Business News
Monday, July 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bankwana Da 2023: Tirka-tirkar Canjin Kudi

by Bello Hamza
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Bankwana Da 2023: Tirka-tirkar Canjin Kudi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sanarwar da Gwamnatin tsohon shugaba Muhammadu Buhari ta sauya wasu takardun kudi tare da fara bayarwa daga ranar 15 ga Dismba, 2022 zuwa 31 ga Janairu, 2023, na daga cikin abubuwan da suka fi daukar hankali a 2023 saboda yadda lamarin ya shafi rayuwar ‘Yan Nijeriya.

Duk da shiga maganar da Majalisar Kasa ta yi na neman Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya tsawaita wa’adin da ya bayar na daina karbar tsofaffin takardar kudin 1000, 500 da 200, Babban Bakin ya ce ba za a kara koda minti daya ba a wa’adin da aka sanya na ranar 31 ga watan Janairu 2023, inda hakan ya sa ‘yan Nijeriya cikin dimuwa. Amma daga bisani da gwamnati ta ji matsin lamba, sai ta kara wa’adin zuwa 11 ga Fabrairu, 2023.

  • Harin Filato: Gwamnati Ba Za Ta Huta Ba Har Sai An Hukunta Maharan – Shettima 
  • NAF Ta Lalata Haramtattun Wuraren Tace Mai Guda 6 A Ribas 

Al’umma sun shiga cikin dimuwa da fargaba. Karancin takardun sabbin kudin da rige-rigen sauyawa a bankuna ya kara haifar da wahalhalu ga ‘yan kasa. Masana sun bayyana cewa, CBN ya samar da sabbin kudin ne na Naira Biliyan 200 kuma abin da ake bukata ya kai fiye da Naira Tiriliyan 3.1 abin da ya sa masana ke ganin shi ne babban dalilin karancin sabbin kudaden.

Masu harkar canjin kudin sun mayar da harkar canjin kasuwanci inda aka rika sayar da sayar da sabbin a unguwar zone 4 da ke babba birnin tayarra Abuja.

Wani karin abin haushi game da canjin kudin shi ne, hanyoyin da ake hada-hadar kudin ta intanet duk sun rika toshewa ta yadda abin ya zama kasada, imma kudin da aka tura ya tafi ko ya salwanta.

Labarai Masu Nasaba

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Ba a wannan karon aka fara canza fasalin kudi a Nijeriya, shugaba Buhari a lokacin da ya jagorancin Nijeriya a matsayin soja a shekara 1983 ya yi canjin kudi wanda ‘yan Nijeriya da dama suka tafka asara sabosa kasa cimma wa’adin mayar da tsofaffin kudin zuwa banki wannan ya sa wadanda suka san irin dambarwar da aka fuskanta a waccan lokacin suka shigta dimuwa da fargabar halin da za a iya shiga in har wa’adin ya kulle mutum bai kai kudinsa banki ba.

Canjin kudi na wannan karon ya zo ne ana tsakiyar hada-hada da gangamin siyasar 2023, kuma kowa yana sane da cewa, harkar siyasa a kasar nan abu ne da ya yake tafiya da kudi, ma’ana iya kudin ka iya shagalin ka

Dimuwa da tashin hankalin da mutane suka shiga sun sa wasu na ikirarin ba za su zabi jam’iyya mai mulki ba, abin da ya sa dan takarar shugaban kasa a jam’iyya mai mulki ta APC Asiwaju Biola Ahmed Tinubu ya bara, ya yi korafin cewa, an kikiro da lamarin tun da farko don kawo masa cikas a yunkurinsa na zama shugaban Nijeriya.

Masu lura da al’amurran yau da kullum sun bayyana cewa, jifar tawagar shugaban kasa a yayin da ya kai ziyara garin Katsina don kaddamar da wasu ayyukan raya kasa da kuma ihun da aka yi a ziyarar kaddamar da wasu ayyukan raya kasa a Jihar Kano, inda wasu yara suka yi jifa da furuce-furucen “Ba ma yi! Bama son canji, da sauransu”, tabbas a bayyane yake cewa, al’amarin canjin ya kara wa gwamnatin Shugaba Buhari bakin jinni.

A wata sabuwa kuma, da yake bayani a wani zauren tattauna wanda wasu shaharrun Lauyoyi da ‘yan Jarida ke gabatarwa a shafin intanet, Manjo Hamza Al-mustapa (Mai Ritaya) ya ce, canjin kudn da aka yi ba komai ba ne illa damfara, yana mai cewa, “419 (Damfara) aka shirya domin a wahalar da ‘yan Nijeriya, idan kuma Emifiele  ya isa, ko shi, ko mukarrabansa su fito fili su karyata in ban tona asiri ba” in shi ji.

Haka kuma Gwamnan JIhar Kaduna Malam Nasir El-Rufai, ya yi zargin cewa, akwai wasu a fadar Shugaban Kasa Muhammadu Buhari da suke neman kayar da dan takarar shugabancin kasa na jam’iyyar APC Asiwaju Bola Ahmed Tinubu a zaben ranar 25 ga watan Fabrairu.

Yanzu haka dai tsohon Gwamnan CBN, Godwin Emefiele na fuskantar tuhuma daban-daban a kan badakalar kudi a gaban kotu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bankwana Da 2023: Radadin Cire Tallafin Mai

Next Post

Bashin Ilimi Ga Daliban Nijeriya: Manufar Da Ba Ta Da Kyakkyawar Manufa

Related

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno
Manyan Labarai

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno

36 minutes ago
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
Manyan Labarai

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

21 hours ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

2 days ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

2 days ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

2 days ago
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

2 days ago
Next Post
Bashin Ilimi Ga Daliban Nijeriya: Manufar Da Ba Ta Da Kyakkyawar Manufa

Bashin Ilimi Ga Daliban Nijeriya: Manufar Da Ba Ta Da Kyakkyawar Manufa

LABARAI MASU NASABA

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno

July 28, 2025
Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Jimamin Rasuwar Babban Ɗan Jarida Leon Usigbe

Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Jimamin Rasuwar Babban Ɗan Jarida Leon Usigbe

July 28, 2025
Ƴansanda Sun Cafke Barayin Motoci 3 A Kano

Ƴansanda Sun Cafke Barayin Motoci 3 A Kano

July 28, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin Bai Wa Malaman Manyan Makarantun Nijeriya Rancen Miliyan 10

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin Bai Wa Malaman Manyan Makarantun Nijeriya Rancen Miliyan 10

July 28, 2025
An Kwashe Duk Dabbobin Tsohon Akanta-Janar

An Kwashe Duk Dabbobin Tsohon Akanta-Janar

July 28, 2025
Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Bincike Kan Belin Dillalin Kwaya

Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Bincike Kan Belin Dillalin Kwaya

July 28, 2025
Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

July 27, 2025
Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

July 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

July 27, 2025
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.