• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bankwana Da 2023: Tirka-tirkar Canjin Kudi

by Bello Hamza
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Bankwana Da 2023: Tirka-tirkar Canjin Kudi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sanarwar da Gwamnatin tsohon shugaba Muhammadu Buhari ta sauya wasu takardun kudi tare da fara bayarwa daga ranar 15 ga Dismba, 2022 zuwa 31 ga Janairu, 2023, na daga cikin abubuwan da suka fi daukar hankali a 2023 saboda yadda lamarin ya shafi rayuwar ‘Yan Nijeriya.

Duk da shiga maganar da Majalisar Kasa ta yi na neman Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya tsawaita wa’adin da ya bayar na daina karbar tsofaffin takardar kudin 1000, 500 da 200, Babban Bakin ya ce ba za a kara koda minti daya ba a wa’adin da aka sanya na ranar 31 ga watan Janairu 2023, inda hakan ya sa ‘yan Nijeriya cikin dimuwa. Amma daga bisani da gwamnati ta ji matsin lamba, sai ta kara wa’adin zuwa 11 ga Fabrairu, 2023.

  • Harin Filato: Gwamnati Ba Za Ta Huta Ba Har Sai An Hukunta Maharan – Shettima 
  • NAF Ta Lalata Haramtattun Wuraren Tace Mai Guda 6 A Ribas 

Al’umma sun shiga cikin dimuwa da fargaba. Karancin takardun sabbin kudin da rige-rigen sauyawa a bankuna ya kara haifar da wahalhalu ga ‘yan kasa. Masana sun bayyana cewa, CBN ya samar da sabbin kudin ne na Naira Biliyan 200 kuma abin da ake bukata ya kai fiye da Naira Tiriliyan 3.1 abin da ya sa masana ke ganin shi ne babban dalilin karancin sabbin kudaden.

Masu harkar canjin kudin sun mayar da harkar canjin kasuwanci inda aka rika sayar da sayar da sabbin a unguwar zone 4 da ke babba birnin tayarra Abuja.

Wani karin abin haushi game da canjin kudin shi ne, hanyoyin da ake hada-hadar kudin ta intanet duk sun rika toshewa ta yadda abin ya zama kasada, imma kudin da aka tura ya tafi ko ya salwanta.

Labarai Masu Nasaba

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Ba a wannan karon aka fara canza fasalin kudi a Nijeriya, shugaba Buhari a lokacin da ya jagorancin Nijeriya a matsayin soja a shekara 1983 ya yi canjin kudi wanda ‘yan Nijeriya da dama suka tafka asara sabosa kasa cimma wa’adin mayar da tsofaffin kudin zuwa banki wannan ya sa wadanda suka san irin dambarwar da aka fuskanta a waccan lokacin suka shigta dimuwa da fargabar halin da za a iya shiga in har wa’adin ya kulle mutum bai kai kudinsa banki ba.

Canjin kudi na wannan karon ya zo ne ana tsakiyar hada-hada da gangamin siyasar 2023, kuma kowa yana sane da cewa, harkar siyasa a kasar nan abu ne da ya yake tafiya da kudi, ma’ana iya kudin ka iya shagalin ka

Dimuwa da tashin hankalin da mutane suka shiga sun sa wasu na ikirarin ba za su zabi jam’iyya mai mulki ba, abin da ya sa dan takarar shugaban kasa a jam’iyya mai mulki ta APC Asiwaju Biola Ahmed Tinubu ya bara, ya yi korafin cewa, an kikiro da lamarin tun da farko don kawo masa cikas a yunkurinsa na zama shugaban Nijeriya.

Masu lura da al’amurran yau da kullum sun bayyana cewa, jifar tawagar shugaban kasa a yayin da ya kai ziyara garin Katsina don kaddamar da wasu ayyukan raya kasa da kuma ihun da aka yi a ziyarar kaddamar da wasu ayyukan raya kasa a Jihar Kano, inda wasu yara suka yi jifa da furuce-furucen “Ba ma yi! Bama son canji, da sauransu”, tabbas a bayyane yake cewa, al’amarin canjin ya kara wa gwamnatin Shugaba Buhari bakin jinni.

A wata sabuwa kuma, da yake bayani a wani zauren tattauna wanda wasu shaharrun Lauyoyi da ‘yan Jarida ke gabatarwa a shafin intanet, Manjo Hamza Al-mustapa (Mai Ritaya) ya ce, canjin kudn da aka yi ba komai ba ne illa damfara, yana mai cewa, “419 (Damfara) aka shirya domin a wahalar da ‘yan Nijeriya, idan kuma Emifiele  ya isa, ko shi, ko mukarrabansa su fito fili su karyata in ban tona asiri ba” in shi ji.

Haka kuma Gwamnan JIhar Kaduna Malam Nasir El-Rufai, ya yi zargin cewa, akwai wasu a fadar Shugaban Kasa Muhammadu Buhari da suke neman kayar da dan takarar shugabancin kasa na jam’iyyar APC Asiwaju Bola Ahmed Tinubu a zaben ranar 25 ga watan Fabrairu.

Yanzu haka dai tsohon Gwamnan CBN, Godwin Emefiele na fuskantar tuhuma daban-daban a kan badakalar kudi a gaban kotu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bankwana Da 2023: Radadin Cire Tallafin Mai

Next Post

Bashin Ilimi Ga Daliban Nijeriya: Manufar Da Ba Ta Da Kyakkyawar Manufa

Related

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Manyan Labarai

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

5 hours ago
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

17 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

19 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

2 days ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

2 days ago
NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja
Manyan Labarai

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

2 days ago
Next Post
Bashin Ilimi Ga Daliban Nijeriya: Manufar Da Ba Ta Da Kyakkyawar Manufa

Bashin Ilimi Ga Daliban Nijeriya: Manufar Da Ba Ta Da Kyakkyawar Manufa

LABARAI MASU NASABA

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.