• English
  • Business News
Monday, August 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Barcelona Ta Dauki Kessie Da Christensen

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
in Wasanni
0
Kessie Da Christensen
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar kwallon kafa ta Barcelona ta cimma yarjejeniyar daukar ‘yan wasa guda biyu, Franck Yannick Kessier, wanda kwantiraginsa ya kare a AC Milan a watan jiya da kuma Andreas Christensen daga Chelsea.

Dan wasa Kessie ya saka hannu kan yarjejeniyar da za ta kare ranar 30 ga watan Yunin shekara ta 2026 haka kuma Barcelona ta sa farashin Yuro miliyan 500 ga duk kungiyar da ke son daukar dan wasan, idan yarjejeniyarsa ba ta kare ba a Camp Nou.

  • Rashford Ya Ce Ya Koma Kan Ganiyarsa

Ranar Laraba 6 ga watan Yuli, Barcelona ta gabatar da Franck Yannick Kessie a matakin dan wasanta kuma an haifi Franck Kessie ranar 19 ga watan Disambar shekarar 1996 a garin Ouragahio da ke Ibory Coast.

Dan wasan mai buga wasa daga tsakiya ko tsaron baya daga tsakiya ya fara wasa a Stella Club d’Adjame ta Ibory Coast daga baya ya koma Atalanta a shekarar 2014 kuma bayan da ya taka rawar gani a kakar wasa ta 2016 zuwa 2017 a Atalanta, daga nan ne AC Milan ta yi zawarcinsa.

Ya koma AC Milan buga wasannin aro a 2017 daga nan ta saye shi a 2019 kan Yuro miliyan 33 kuma tsawon kakar was biyar da Kessie ya yi a Milan ya kara samun gogewa, ya kuma ci kwallaye, ya kuma bayar an zura a raga.

Labarai Masu Nasaba

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

Dan wasan tawagar Ibory Coast ya taimakawa AC Milan ta dauki Serie A a kakar da aka karkare, kofin farko da ta dauka tun bayan kakar wasa 11. Har ila yau, Barcelona ta sanar da daukar dan wasa Andreas Christensen daga Chelsea, bayan da kwantiraginsa shi ma ya kare a Stamford Bridge a karshen watan Yuni kuma Christensen ya amince da kunshin yarjejeniyar.

kaka hudu da saka farashin Yuro miliyan 500 ga duk kungiyar da ke son daukarsa, idan wa’adinsa bai kare ba a Camp Nou.
Dan kwallon ya koma Chelsea daga Brondby a shekarar 2012, wanda kaka biyu tsakani ya fara buga wasa a matakin kwararren dan wasa sai dai Chelsea ta bayar da aron dan wasan kaka biyu ga Borussia Monchengladbach, sai dai tun da ya koma Chelsea ya nuna kansa.

Ya buga wa kungiyar wasanni 167 har da 26 da ya yi a kakar da ta wuce da cin kwallo hudu kuma dan kwallon ya lashe Champions League da Europa League da Club World Cup da kuma UEFA Super Cup a wasannin da ya yi wa kungiyar Stamford Bridge.

Haka kuma Chelsea ta yi nasarar cin wasanni 92 a karawar da Christensen ya buga mata sai dai Bayan da Barcelona ta kammala daukar Christensen da Kessie, kungiyar za ta mayar da hankali kan zawarcin Raphinha na Leeds United.

Haka kuma Barcelona na tattaunawa da Ousmane Dembele kan tsawaita zamansa a Camp Nou, bayan da yarjejeniyar dan kwallon tawagar Faransa ta kare a kungiyar kuma tuni dai Manchester United ke ta kokarin ganin ta kammala sayen dan wasan Barcelona, Frenkie de Jong kafin fara kakar bana da za a yi a cikin watan Agusta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Lauya Ya Koka Kan Jinkiri Wajen Yanke Hukunci A Kotuna

Next Post

Saboda Guardiola Na Koma Manchester City, Cewar Phillips

Related

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig
Wasanni

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

2 days ago
Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham
Wasanni

Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

2 days ago
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace
Wasanni

Jerin Ƴan Wasa Mata Da Suka Samu Kyautar Dala 100,000 Daga Gwamnatin Nijeriya

2 days ago
UEFA Ta Ci Tarar Lamine Yamal Da Lewandowski Kan Karya Dokar Shan Ƙwayar Ƙara Kuzari
Wasanni

UEFA Ta Ci Tarar Lamine Yamal Da Lewandowski Kan Karya Dokar Shan Ƙwayar Ƙara Kuzari

3 days ago
Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 
Wasanni

Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 

3 days ago
Al Hilal Za Ta Biya Yuro Miliyan 53 Don Ɗaukar Nunez Daga Liverpool
Wasanni

Al Hilal Za Ta Biya Yuro Miliyan 53 Don Ɗaukar Nunez Daga Liverpool

4 days ago
Next Post
Phillips

Saboda Guardiola Na Koma Manchester City, Cewar Phillips

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

August 11, 2025
Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

August 10, 2025
Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

August 10, 2025
Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

August 10, 2025
INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

August 10, 2025
Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK

Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK

August 11, 2025
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

August 10, 2025
Sin Ta Gudanar Da Gwajin Farko Na Gagarumin Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Dakarun Japan

Sin Ta Gudanar Da Gwajin Farko Na Gagarumin Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Dakarun Japan

August 11, 2025
Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

August 10, 2025
Sin Na Gaggauta Gina Tsarin Tattalin Arziki Mai Kiyaye Muhallin Halittu

Sin Na Gaggauta Gina Tsarin Tattalin Arziki Mai Kiyaye Muhallin Halittu

August 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.