• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bashin Naira Biliyan 2.5: Duhu Ya Mamaye Ma’aikatun Sakkwato Da Zamfara

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
3 years ago
Zamfara

Ma’aikatu da Hukumomin Gwamnatocin Jihohin Sakkwato da Zamfara sun kasance a cikin duhu bakidaya a yayin da Hukumar Wutar Lantarki ta Kaduna (KEDCO) ta tsinke layukan wutar a dalilin dimbin bashi.

Kamfanin KEDCO ya bayyana cewar ba ya da wani zabi face daukar matakin yanke wutar bayan cikar wa’adin makwanni uku da suka baiwa Gwamnatocin domin su biya tarin bashin da kamfanin ke bin su ko su saka su a duhu.

  • Gina Al‘ummar Sin Da Afirka Mai Koshin Lafiya Ba Batu Ne Na Fatar Baki Ba 
  • An Raba Wa Jami’an Tsaro Na NSCDC 7 Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe Cakin Banki Da Guraben Aiki

Shugaban sashen Yada Labarai na KEDCO Abdul’aziz Abdallah a sanarwar da ya fitar makon jiya ya bayyana cewar kamfanin na bin Gwamnatin Jihar Sakkwato tsabar kudi naira biliyan 1, 496, 313, 156 a yayin da Gwamnatin Zamfara ke rike da bashin kamfanin na naira biliyan 1, 040, 506, 740 daga watan Disamba 2022.

Yanke layukan ya haifar da tarin illoli da dama a Ma’aikatu da Hukumomin Gwamnatocin biyu kasancewar ayyukan yau da kullum na gudanar da ofisoshi da dama sun tsaya, wasu kuma ba su tafiya yadda ya kamata.

A wasu ma’aikatu ba su da zabi face amfani da injinin janareta domin haskaka ma’aikatun da kuma aiwatar da ayyukan da suka wajaba a gare su.

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Sanarwar ta bayyana cewar yanke wutar shine mataki na karshe da za su iya dauka musamman saboda rashin biyan bashin wanda KEDCO ta bayyana cewar ba wai hakan na kawo masu cikas wajen aiwatar da ayyukan su ne kawai ba, yana kuma zamar masu matukar wahala wajen sauke nauyin da ke kan su na baiwa al’umma haske da kuma samun ribar da za su kara inganta ayyukan su.

“Abin damuwa ne yadda Gwamnatin Zamfara ta kasa biyan kudin wuta a tsawon watanni 12 da suka gabata a yayin da Jihar Sakkwato ta kasa biyan wuta na tsawon watanni hudu.”

Bayanin ya nuna cewar Hukumar KEDCO ta dauki matakin bayar sanar da Gwamnatocin bukatar biyan basukan da kuma notis na karshe bayan da dukkanin alkawulan da suka dauka na biyan kudaden ya faskara duk da an yi ta tunatarwa.

Kamfanin na KEDCO ya bayyana cewar ya wajaba ga kamfanin su rika biyan kashi 100 na wutar da suke karba da na gudanarwa wanda akwai hukunci idan suka saba wanda a kan hakan kamfanin ya ce wannan dalilin ne ya sa suke fadi tashi a kowane wata amma abin kan faskara saboda karanci, rashin biya da biyan wuta ba bisa ka’ida ba.

“Muna bayar da tabbacin cewar a shirye muke mu mayar da hasken wuta a ma’aikatun Gwamnatocin biyu da muka yanke idan aka dauki matakan da ya kamata na biyan dadadden bashin da kuma tabbacin ci-gaba da biyan wuta yadda ya kamata a cikin lokaci.” In ji kamfanin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta
Manyan Labarai

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin
Manyan Labarai

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Next Post
Masarautar Katsina Ta Warware Rawanin Hakimin Bakori, Makaman Katsina

Masarautar Katsina Ta Warware Rawanin Hakimin Bakori, Makaman Katsina

LABARAI MASU NASABA

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.